• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Hukumar NOA Ta Tsunduma Gangamin Tara Wa Super Eagles Ɗimbin Magoya Baya – Minista

by Sulaiman
2 years ago
AFCON

Yayin da ake ta shirye-shiryen karawa tsakanin ƙungiyar Super Eagles ta Nijeriya da Elephants ta Ivory Coast a wasan ƙarshe na Gasar Cin Kofin Afirka na bana (AFCON 2023), tuni Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar Da da Kai ta Ƙasa (NOA) ta fara gangamin tara wa ‘yan wasan Nijeriya ɗimbin magoya baya a dukkan jihohin ƙasar nan.

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce ma’aikatarsa za ta raba wa jama’a dubunnan tutocin Nijeriya a wuraren kallon ƙwallon ƙafa a faɗin ƙasar nan.

  • AFCON: Mai Yi Wa Kasa Hidima Ya Rasu Yayin Kallon Wasan Nijeriya Da Afrika Ta Kudu A Adamawa
  • AFCON 2023: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Gwamnatin Nijeriya Zuwa Kallon Wasan Karshe

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Ministan, Malam Rabi’u Ibrahim ya fitar, ya ce tuni NOA ta fara wannan gagarumin aikin domin ɗabbaƙa ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi a shirin farfaɗo da kishin ƙasa a zukatan ‘yan Nijeriya.

Ya ce hakan kuma wani hoɓɓasa ne da zai ƙara wa ‘yan wasan Nijeriya ƙwarin gwiwar kaiwa ga nasarar ɗaukar kofi.

Za a buga wannan wasa a yau Lahadin a Dandalin Alassane Quattara da ke Abidjan, babban birnin Ivory Coast, ƙasar da ta ɗauki baƙuncin shirya gasar.

LABARAI MASU NASABA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Idris ya ce, “Tutar ƙasa na ɗaya daga cikin tambarin da kowace ƙasa ke tutiya da shi, domin ita ce madubin hangen nesan shirin wannan gwamnati na wayar da kai da cusa ɗa’a da kyawawan ɗabi’u a dukkan al’amurran tafiyar da rayuwar mu.

“To, yau babbar rana ce da mu ka samu muhimmiyar damar nuna wannan kishi da kuma kyakkyawan ƙudiri na wannan gwamnatin ga ‘yan Nijeriya.”

Ministan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya mazauna Ivory Cost cewa su yi fitar farin ɗango zuwa filin wasan domin nuna wa ‘yan wasan mu goyon baya da kuma nuna kishi ga ƙasa.

Ya ce Shugaba Bola Tinubu ya gamsu sosai da irin takun wasan da Super Eagles su ka yi a yayin karawar su da ƙungiyoyin ƙasashe daban-daban.

Ya ce kuma ya na da ƙwarin gwiwar cewa nasara na tare da Nijeriya.

Ya ce: “Gwamnati na da ƙwarin gwiwar cewa ‘yan wasan Super Eagles ne za su yi nasarar ɗaukar kofin na AFCON, wanda hakan zai kasance na huɗu kenan da Nijeriya za ta ɗauka. Kuma duk wani irin goyon baya da buƙatun da ƙungiyar ta nema, tuni ta samu daga gwamnati, domin dai a ƙarfafa masu gwiwa don kaiwa ga nasarar ɗaukar Kofin Afrika.”

Kafin Nijeriya ta kai ga wasan ƙarshen na yau dai sai da ta lallasa Afrika ta Kudu da ci 4:2 a bugun daga kai sai gola, a wasan kusa da na ƙarshe, bayan an tashi wasan 1:1.

Wannan nasara da Nijeriya ta samu, ta ƙara wa ‘yan ƙasa karsashin kishi a zukatan su sosai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana
Wasanni

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars
Wasanni

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta
Labarai

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana

LABARAI MASU NASABA

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

October 23, 2025
Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

October 23, 2025
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.