ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Hukumar NOA Ta Tsunduma Gangamin Tara Wa Super Eagles Ɗimbin Magoya Baya – Minista

by Sulaiman
2 years ago
AFCON

Yayin da ake ta shirye-shiryen karawa tsakanin ƙungiyar Super Eagles ta Nijeriya da Elephants ta Ivory Coast a wasan ƙarshe na Gasar Cin Kofin Afirka na bana (AFCON 2023), tuni Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar Da da Kai ta Ƙasa (NOA) ta fara gangamin tara wa ‘yan wasan Nijeriya ɗimbin magoya baya a dukkan jihohin ƙasar nan.

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce ma’aikatarsa za ta raba wa jama’a dubunnan tutocin Nijeriya a wuraren kallon ƙwallon ƙafa a faɗin ƙasar nan.

  • AFCON: Mai Yi Wa Kasa Hidima Ya Rasu Yayin Kallon Wasan Nijeriya Da Afrika Ta Kudu A Adamawa
  • AFCON 2023: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Gwamnatin Nijeriya Zuwa Kallon Wasan Karshe

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Ministan, Malam Rabi’u Ibrahim ya fitar, ya ce tuni NOA ta fara wannan gagarumin aikin domin ɗabbaƙa ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi a shirin farfaɗo da kishin ƙasa a zukatan ‘yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya ce hakan kuma wani hoɓɓasa ne da zai ƙara wa ‘yan wasan Nijeriya ƙwarin gwiwar kaiwa ga nasarar ɗaukar kofi.

Za a buga wannan wasa a yau Lahadin a Dandalin Alassane Quattara da ke Abidjan, babban birnin Ivory Coast, ƙasar da ta ɗauki baƙuncin shirya gasar.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Idris ya ce, “Tutar ƙasa na ɗaya daga cikin tambarin da kowace ƙasa ke tutiya da shi, domin ita ce madubin hangen nesan shirin wannan gwamnati na wayar da kai da cusa ɗa’a da kyawawan ɗabi’u a dukkan al’amurran tafiyar da rayuwar mu.

“To, yau babbar rana ce da mu ka samu muhimmiyar damar nuna wannan kishi da kuma kyakkyawan ƙudiri na wannan gwamnatin ga ‘yan Nijeriya.”

Ministan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya mazauna Ivory Cost cewa su yi fitar farin ɗango zuwa filin wasan domin nuna wa ‘yan wasan mu goyon baya da kuma nuna kishi ga ƙasa.

Ya ce Shugaba Bola Tinubu ya gamsu sosai da irin takun wasan da Super Eagles su ka yi a yayin karawar su da ƙungiyoyin ƙasashe daban-daban.

Ya ce kuma ya na da ƙwarin gwiwar cewa nasara na tare da Nijeriya.

Ya ce: “Gwamnati na da ƙwarin gwiwar cewa ‘yan wasan Super Eagles ne za su yi nasarar ɗaukar kofin na AFCON, wanda hakan zai kasance na huɗu kenan da Nijeriya za ta ɗauka. Kuma duk wani irin goyon baya da buƙatun da ƙungiyar ta nema, tuni ta samu daga gwamnati, domin dai a ƙarfafa masu gwiwa don kaiwa ga nasarar ɗaukar Kofin Afrika.”

Kafin Nijeriya ta kai ga wasan ƙarshen na yau dai sai da ta lallasa Afrika ta Kudu da ci 4:2 a bugun daga kai sai gola, a wasan kusa da na ƙarshe, bayan an tashi wasan 1:1.

Wannan nasara da Nijeriya ta samu, ta ƙara wa ‘yan ƙasa karsashin kishi a zukatan su sosai.

AFCON
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.