• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Hukumar NOA Ta Tsunduma Gangamin Tara Wa Super Eagles Ɗimbin Magoya Baya – Minista

by Sulaiman
2 years ago
AFCON

Yayin da ake ta shirye-shiryen karawa tsakanin ƙungiyar Super Eagles ta Nijeriya da Elephants ta Ivory Coast a wasan ƙarshe na Gasar Cin Kofin Afirka na bana (AFCON 2023), tuni Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar Da da Kai ta Ƙasa (NOA) ta fara gangamin tara wa ‘yan wasan Nijeriya ɗimbin magoya baya a dukkan jihohin ƙasar nan.

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce ma’aikatarsa za ta raba wa jama’a dubunnan tutocin Nijeriya a wuraren kallon ƙwallon ƙafa a faɗin ƙasar nan.

  • AFCON: Mai Yi Wa Kasa Hidima Ya Rasu Yayin Kallon Wasan Nijeriya Da Afrika Ta Kudu A Adamawa
  • AFCON 2023: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Gwamnatin Nijeriya Zuwa Kallon Wasan Karshe

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Ministan, Malam Rabi’u Ibrahim ya fitar, ya ce tuni NOA ta fara wannan gagarumin aikin domin ɗabbaƙa ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi a shirin farfaɗo da kishin ƙasa a zukatan ‘yan Nijeriya.

Ya ce hakan kuma wani hoɓɓasa ne da zai ƙara wa ‘yan wasan Nijeriya ƙwarin gwiwar kaiwa ga nasarar ɗaukar kofi.

Za a buga wannan wasa a yau Lahadin a Dandalin Alassane Quattara da ke Abidjan, babban birnin Ivory Coast, ƙasar da ta ɗauki baƙuncin shirya gasar.

LABARAI MASU NASABA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

Idris ya ce, “Tutar ƙasa na ɗaya daga cikin tambarin da kowace ƙasa ke tutiya da shi, domin ita ce madubin hangen nesan shirin wannan gwamnati na wayar da kai da cusa ɗa’a da kyawawan ɗabi’u a dukkan al’amurran tafiyar da rayuwar mu.

“To, yau babbar rana ce da mu ka samu muhimmiyar damar nuna wannan kishi da kuma kyakkyawan ƙudiri na wannan gwamnatin ga ‘yan Nijeriya.”

Ministan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya mazauna Ivory Cost cewa su yi fitar farin ɗango zuwa filin wasan domin nuna wa ‘yan wasan mu goyon baya da kuma nuna kishi ga ƙasa.

Ya ce Shugaba Bola Tinubu ya gamsu sosai da irin takun wasan da Super Eagles su ka yi a yayin karawar su da ƙungiyoyin ƙasashe daban-daban.

Ya ce kuma ya na da ƙwarin gwiwar cewa nasara na tare da Nijeriya.

Ya ce: “Gwamnati na da ƙwarin gwiwar cewa ‘yan wasan Super Eagles ne za su yi nasarar ɗaukar kofin na AFCON, wanda hakan zai kasance na huɗu kenan da Nijeriya za ta ɗauka. Kuma duk wani irin goyon baya da buƙatun da ƙungiyar ta nema, tuni ta samu daga gwamnati, domin dai a ƙarfafa masu gwiwa don kaiwa ga nasarar ɗaukar Kofin Afrika.”

Kafin Nijeriya ta kai ga wasan ƙarshen na yau dai sai da ta lallasa Afrika ta Kudu da ci 4:2 a bugun daga kai sai gola, a wasan kusa da na ƙarshe, bayan an tashi wasan 1:1.

Wannan nasara da Nijeriya ta samu, ta ƙara wa ‘yan ƙasa karsashin kishi a zukatan su sosai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
Wasanni

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid
Wasanni

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.