• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Hukumar NOA Ta Tsunduma Gangamin Tara Wa Super Eagles Ɗimbin Magoya Baya – Minista

by Sulaiman
1 year ago
in Wasanni
0
AFCON 2023: Hukumar NOA Ta Tsunduma Gangamin Tara Wa Super Eagles Ɗimbin Magoya Baya – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ake ta shirye-shiryen karawa tsakanin ƙungiyar Super Eagles ta Nijeriya da Elephants ta Ivory Coast a wasan ƙarshe na Gasar Cin Kofin Afirka na bana (AFCON 2023), tuni Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar Da da Kai ta Ƙasa (NOA) ta fara gangamin tara wa ‘yan wasan Nijeriya ɗimbin magoya baya a dukkan jihohin ƙasar nan.

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce ma’aikatarsa za ta raba wa jama’a dubunnan tutocin Nijeriya a wuraren kallon ƙwallon ƙafa a faɗin ƙasar nan.

  • AFCON: Mai Yi Wa Kasa Hidima Ya Rasu Yayin Kallon Wasan Nijeriya Da Afrika Ta Kudu A Adamawa
  • AFCON 2023: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Gwamnatin Nijeriya Zuwa Kallon Wasan Karshe

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Ministan, Malam Rabi’u Ibrahim ya fitar, ya ce tuni NOA ta fara wannan gagarumin aikin domin ɗabbaƙa ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi a shirin farfaɗo da kishin ƙasa a zukatan ‘yan Nijeriya.

Ya ce hakan kuma wani hoɓɓasa ne da zai ƙara wa ‘yan wasan Nijeriya ƙwarin gwiwar kaiwa ga nasarar ɗaukar kofi.

Za a buga wannan wasa a yau Lahadin a Dandalin Alassane Quattara da ke Abidjan, babban birnin Ivory Coast, ƙasar da ta ɗauki baƙuncin shirya gasar.

Labarai Masu Nasaba

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Idris ya ce, “Tutar ƙasa na ɗaya daga cikin tambarin da kowace ƙasa ke tutiya da shi, domin ita ce madubin hangen nesan shirin wannan gwamnati na wayar da kai da cusa ɗa’a da kyawawan ɗabi’u a dukkan al’amurran tafiyar da rayuwar mu.

“To, yau babbar rana ce da mu ka samu muhimmiyar damar nuna wannan kishi da kuma kyakkyawan ƙudiri na wannan gwamnatin ga ‘yan Nijeriya.”

Ministan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya mazauna Ivory Cost cewa su yi fitar farin ɗango zuwa filin wasan domin nuna wa ‘yan wasan mu goyon baya da kuma nuna kishi ga ƙasa.

Ya ce Shugaba Bola Tinubu ya gamsu sosai da irin takun wasan da Super Eagles su ka yi a yayin karawar su da ƙungiyoyin ƙasashe daban-daban.

Ya ce kuma ya na da ƙwarin gwiwar cewa nasara na tare da Nijeriya.

Ya ce: “Gwamnati na da ƙwarin gwiwar cewa ‘yan wasan Super Eagles ne za su yi nasarar ɗaukar kofin na AFCON, wanda hakan zai kasance na huɗu kenan da Nijeriya za ta ɗauka. Kuma duk wani irin goyon baya da buƙatun da ƙungiyar ta nema, tuni ta samu daga gwamnati, domin dai a ƙarfafa masu gwiwa don kaiwa ga nasarar ɗaukar Kofin Afrika.”

Kafin Nijeriya ta kai ga wasan ƙarshen na yau dai sai da ta lallasa Afrika ta Kudu da ci 4:2 a bugun daga kai sai gola, a wasan kusa da na ƙarshe, bayan an tashi wasan 1:1.

Wannan nasara da Nijeriya ta samu, ta ƙara wa ‘yan ƙasa karsashin kishi a zukatan su sosai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adadin kyaututtukan tawagar Super EaglesAhmed MusaHasashen wasan karshe na AFCON 2023Tarihin AFCON
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana’antar Samar Da Kayayyaki Ta Kasar Sin Ta Samu Farfadowa A Shekarar 2023

Next Post

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Related

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

2 days ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

3 days ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

4 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

5 days ago
Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 
Wasanni

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

5 days ago
Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi
Wasanni

Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi

6 days ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.