• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
Amurka

Shugaban Amurka Donald Trump ya riga ya kwashe watanni shida yana mulki a ƙasarsa. Ayyukan da ya yi a waɗannan watanni sun bayyanawa ƙasashen Afirka ƙarara cewa, Afirka ba ta cikin jerin fannoni da ƙasar Amurka ta bai wa fifiko.

Idan aka kwatanta da wa’adin shugaba Trump na farko, wanda ya ƙunshi yadda ya yi wa ƙasashen Afirka wulaƙanci ta hanyar kiransu da laƙabai marasa daɗin ji, da rashin kulawa da ya nuna wa nahiyar (ya gana da shugabannin ƙasashen Afirka biyu kaɗai, kuma bai taɓa ziyartar Afirka ba), shugaba Trump ya ƙara ɗaukar matakai kan Afirka a wa’adinsa na biyu.

  • Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
  • Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Misali, ya rufe Hukumar Raya Ƙasashen Duniya ta Amurka (USAID), tare da rage yawan tallafin da ƙasar take bai wa Afirka. Ya kuma bayyana shirinsa na soke shirin ƙasarsa na tallafa wa ƙoƙarin yaƙi da cutar kanjamau a duniya (PEPFAR), duk da cewa lamarin zai iya haddasa asarar miliyoyin rayuka a Afirka.

Kazalika, manufar karɓar karin harajin fito da shugaba Trump ya ƙaddamar za ta ƙara wa ƙasashen Afirka nauyi sosai. Kana wani umurnin da ya saka masa hannu a baya-bayan nan shi ne taƙaita damar ‘yan ƙasashen Afirka bakwai, ciki har da Najeriya da Kamaru, ta fuskar bizar zuwa Amurka.

Afirka ta Kudu yana ɗaya daga cikin ƙasashen Afirka da suka fuskanci matsin lamba na musamman daga Shugaba Trump: Amurka ta kori jakadanta, kuma manyan jami’an Ƙasar Amurka sun kaucewa dukkan taruka masu alaƙa da G20, da Afirka ta Kudu ta karɓi baƙunci. Ban da haka, ganawar da shugaba Trump ya yi da shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ma ta riƙide, har ta zama tamkar cacar baka a wani lokaci. Abubuwan da aka yi tababa a kai sun haɗa da zargin da Amurka ɗin ta yi wa Afirka ta Kudu, cewa wai tana yi wa al’ummarta ‘yan asalin Turai “kisan kiyashi”, da yadda Afirka ta Kudu ta kasance mamba a ƙungiyar BRICS, da kuma yadda ƙasar ke ɗora muhimmanci kan batun sauyin yanayi a lokacin da take shugabancin ƙungiyar G20.

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Ganawar da shugaba Trump ya yi a baya-bayan nan da shugabannin wasu ƙasashe biyar dake nahiyar Afirka, ita ma ta janyo hankalin al’ummun duniya. Inda shugaba Trump ya yabawa shugaban ƙasar Laberiya Joseph Boakai kan yadda ya iya Turancin Ingilishi sosai, lamarin da ya bayyana rashin fahimtarsa kan alaƙar tarihi tsakanin ƙasar Laberiya da Amurka. Bugu da ƙari, Trump ya katse maganar shugaban Ƙasar Mauritaniya Mohammed Ghazouani, inda ya nemi ya yi magana da sauri.

A hakika, rashin mutuntawa da shugaba Trump ya nuna a fili, ta bayyana ainihin dalilin da ya sa aka gayyaci shugabannin Afirka biyar zuwa wajen ganawar, ba domin neman ƙarfafa dangantaka ba ne, sai dai don tabbatar wa Amurka ɗin damar samun ma’adanan da take buƙata, da yiwuwar sanya waɗannan ƙasashen dake nahiyar Afirka amincewa da karɓar baƙin haure da ake korarsu daga Amurka.

Wataƙila, shugaba Trump ba ya mai da hankali sosai kan ɗa’a a fannin diflomasiyya, amma idan aka kwatanta da shugabannin ƙasar Amurka da suka gabace shi, to, a ƙalla yana bayyana komai a fili ba tare da rufa-rufa ba.

Maganarsa da matakan da ya ɗauka, dukkansu na isar da saƙo zuwa ga ƙasashen Afirka cewa: “Ba ku cikin jerin fannonin da Amurka take nunawa fifiko.”

“Za mu iya musayar wasu abubuwa, amma kada ku yi tsammanin za ku samu riba ko alfanu sosai.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga
Kasashen Ketare

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Next Post
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.