• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Gina Babbar Mayankar Dabbobi Zai Taimaka Wajen Kara Samar Da Wadataccen Nama A Nijeriya – Minista

byAbubakar Abba and Sulaiman
8 months ago
Mayankar dabbobi

Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwo, Idi Mukhtar Maiha ya bayyana cewa, aikin gina mayankar dabbobi ta rukunin kamfanonin ABIS da ke Abuja, baya ga taimakawar da za ta yi wajen sarrafa Nama, za kuma ta taimaka wajen samar da ilimi a fadin kasar nan.

Da zarar an kammala aikin mayankar, za ta taimaka wajen kara bayar da dama a bangaren zuba hannun jari tare kuma da tallafa wa mayankar da ke Jihar Legas, wajen sarrafa Naman Shanu 200 a kowace rana da sarrafa Naman Kajin gidan gona 15,000 da kuma sarrafa tan 100 na Kifi.

  • Abin Da Ya Sa Masu Ruwa Da Tsaki Suka Gana Da Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur
  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Taron Koli Kan Fasahar AI A Faransa

Kazalika, idan an kammala mayankar,  za a iya sarrafa Shanu 1,000 tare da samar da tan daga 400 zuwa 600 na Kajin gidan gona da Awaki 2,000 da Raguna tan 1,000 na Kifi da sauran makamantansu.

Wannan zuba hannun jari na dala miliyan 30, zai samar da ayyukan yi na kai tsaye kimanin 1,000, tare kuma da samar da ayyukan yi wadanda ba na kai tsaye ba, sama da 20,000 a fannin kiwo a wannan kasa.

Maiha, a jawabinsa lokacin da ya kai ziyarar aiki ga mayankar ta  ABIS da ke yankin Idu a Abuja, ya sanar da cewa; karancin da ake da shi na kwararrun masu kula da fannin kiwon dabobi a kasar, nan ba da jimawa ba; zai zama tarihi.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

A cewar Maiha, kafa wajen bayar da horo da kamfanin na ABIS ya yi, zai cike gibin da ake da shi a fannin kiwo da kuma bayar da gudunmawa wajen kara habaka tattalin arzikin fannin.

Ministan ya kara da cewa, bayar da ingantaccen horo a fannin bunkasa kiwo, zai taimaka wajen samar da wadataccen abinci da kara samar da ayyukan yi ga ‘yan kasar, musamman ma matasa.

Maiha, ya kuma bai wa kamfanin na ABIS tabbacin cewa, ma’aikatarsa, za ta bai wai kamfanin goyon bayan da ya dace, domin samar da kwararru a fannin bunkasa kiwon kasar.

Da yake yin tsokaci kan jajircewa da mayar da hankali na kamfanin na ABIS, Maiha ya bukaci kamfanin ya yi hadaka da ma’aikatarsa, musamman domin cimma burin da ya sanya a gaba na sarrafa Nama a kasar.

Ya kuma jaddada cewa, fannin kiwo na matukar taimakawa wajen samar da ayyukan yi da kuma kara habaka tattalin arzikin kasa.

Shi kuwa a nasa jawabin, Shugaban  kamfanin na ABIS, Jakada Emmanuel Nelson Usman ya bayyana cewa, an kafa kamfanin ne, domin yin amfani da kimiyyar zamani; wajen sarrafa Nama a kasar.

Ya sanar da cewa, ta hanyar kamfanin; za a iya samar da ayyukan yi na kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba ga ‘yan kasar, wanda hakan zai taimaka wajen kara habaka tattalin arzikin kasar da kuma kara samar da wadataccen abinci a Nijeriya.

Nelson, ya kuma bukaci taimako daga Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon, musamman a bangaren sahalewar shigo da sundukan kamfanin da ke dauke da kayan kamfanin ta hanyar tashoshin jiragen ruwa na kasa, musamman don kamfanin ya samu damar kafa makarantar koyar da kiwon dabbobi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Cinikayyar ‘Yan Kwallon Da Aka Yi A Watan Janairu

Cinikayyar ‘Yan Kwallon Da Aka Yi A Watan Janairu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version