ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa

by Abubakar Abba
9 months ago
Jigawa

Sama da shekaru biyu da suka gabata, masu yin dokoki da jagorori da manoma da kungiyoyi masu zaman kansu da kuma sauran masu ruwa da tsaki a fannin noma, ke ci gaba da yin tsokaci kan tsarin bunkasa fannain noma na Jihar Jigawa.

A makon da ya gabata ne, Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima, ya yi karin haske kan wannan tsari na noma, wanda kuma ya danganta shi a matsayin wani mataki na kara wanzar da zaman lafiya a jihar ta Jigawa da kuma daukacin fadin kasar baki-daya.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Yadda Mutanen Gari Suka Lakaɗa Wa Ɗan Majalisa Duka A Zamfara

Kashim ya je Jigawa ne, domin taya mai martaba Sarkin Gumel, Dakta Ahmad Muhammad Sani, muranr cika shekara 45, kan karagar mulkin masarautarsa.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ya danganta saukin da ake ci gaba da samu a fannin tsaro na jihar, kan ci gaba da samar da sauye-sauyen da gwamnatin jihar ke ci gaba da yi a fannin noma na jihar.

Hatta shi ma, Babban Ministan Ma’aiktar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Abubakar Kyari, na yawan kai ziyarar aiki jihar ta Jigawa, inda yake nuna sha’awarsa kan tsarin na aikin noma, wanda Jigawa ta kirkiro a karkashin jagorancin Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Wannan tsarin, ya wuce batun a takarda kadai, domin ana gudanar da shi ne, a aikace da kuma jingine batun siyasa a gefe guda, wanda hakan ya sanya Ministan ya ayyana Jigawa a matsayin jihar da za a iya samar da wadatacen abinci a kasar nan.

Gwamnan Jigawa Malam Umar Namadi, ya kirkiro da tsarin cikin kudurorin gwamnatinsa guda 12, wanda hakan ya sanya abokan hadaka da dama suka samar da dauki a cikin tsarin.

Aboan hadakar, sun kasance suna bayar da tallafin kudade, musamman domin a kara habaka noman da manoman Jigawa ke yi.

Koda-yake dai, Jigawa ta kasance tana fuskantar kalubalen sauyin yanayi da zaizayar kasar noma da ambaliyar ruwan sama, amma duk da haka; wannan tsarin ya dan samar da sauki kan wadannan matsaloli.

A hirarsa da manema labarai, Shettima ya nuna jin dadinsa kan sakamako mai kyau da tsarin ya samar a fannin noman jihar.

Kazalika, ya yaba da kokarin da gwamnonin jihohi 36 na kasar nan ke ci gaba da yi na ganin an samar da wadataccen abinci a kasar.

Ya kuma yaba kan samar da wannan tsari, wanda ya sanar da cewa; tsarin zai kara taimakawa wajen kara samar da ayyukan yi da yaki da talauci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin kasar.

Shettima ya jinjina kan yadda jihar ta kara habaka noman Alkama, musamman daga hekta 30,000 zuwa sama da hekta 110,000, a cikin shekaru biyu da kuma yadda jihar ke da burin samar da wasu hekta 500,000, nan da shekaru biyar masu zuwa.

Bugu da kari, a karkashin tsarin na Gwamna Namadi, an gyara dubban hektar noma tare da bai wa manoman jihar damar yin nomansu.

Gwamnatin ta kuma gyara sabbin guraren da za a yi noman rani, ciki har da kamar na yankin Lallashi da ke Karamar Hukumar Maigatari.

Ta kuma ayyana ci gaba da bai wa manoma daukin kudaden yin nom ba tare da bata wani lokaci ba, ciki har da noman Shinkafa, domin jawo hankalin wadanda suke a jihar da suka kammala manyan makarantu, domin shiga fannin na yin noma a matsayin samun kudaden shiga, domin samun riba.

Haka zalika, gwamnatin ta samar da kayan aikin noma na zamani kan farashai mai sauki tare da kuma kara daukar malaman gona daga 300 zuwa 2,000, wanda hakan ya kara habaka fannin a jihar.

Bugu da kari, gwamnatin ta kuma kara bunkasa fannin kiwon dabbobi da kiwon kajin gidan gona, inda kuma ta dauki kwararrun likitocin dabbobi 300.

Ta yi hakan ne, bisa hadaka da wani gidan gona na kasar Indiya da nufin samar da abincin dabbobin da na kajin gidan gona ta yadda za a dakile yaduwar cututtuka tsakanin dabbobin da samar da wajen yin kiwo.

Haka zalika, a karkashin tsarin an samar da cibiyoyin zamani shida na bayar da horo a mazabu 30 na jihar.

An kuma horas da daliban da suka kammala manayn makarantu 30 da suka samu takardar sheda a fannin kiwon aikin Injiya a Kasar China tare kuma da horas da wasu.

Sun fara gudanar da gwajin ilimin da suka samo a kasar ne, bayan sun koma Jigawa, inda suka harhada taraktocin noma da sauran kayan aikin noma da gwamnatin Jigawa ta shigo da su.

A yanzu haka, daukacin al’ummar jihar na jiran ganin ranar da za a kaddamar da wadannan dubban kayan aikin noma da za a yi amfani da su a jihar, inda suke da yakinin kayan za su samar da kyakkyawan sauyi ga fannin aikin noma na Jigawa.

Jigawa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
An Bukaci Amurka Da Ta Kauracewa Sanya Wasu Sassa Na Muzgunawa Kasar Sin Cikin Kudurin Dokar Tsaron Kasa

An Bukaci Amurka Da Ta Kauracewa Sanya Wasu Sassa Na Muzgunawa Kasar Sin Cikin Kudurin Dokar Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.