• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Hada Hannu Domin Kyautata Dangantakarsu

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar harkokin wajen Sin ta ce kasar na fatan Amurka za ta cika alkawarin da ta yi cewa, ba ta neman sabon yakin cacar baka ko rikici da kasar Sin, kuma za ta hada hannu da Sin din wajen mayar da huldarsu bisa turbar da ta dace.

Kakakin ma’aikatar Mao Ning ce ta bayyana haka a jiya, yayin da take amsa tambaya game da ganawar shugabannin kasashen biyu dake tafe.

  • Xi Jinping Ya Tashi Zuwa Kasar Amurka Domin Gudanar Da Taron Shugabannin Kasashen Sin Da Amurka Da Taron APEC Karo Na 30
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Shekara-shekara Na ’Yan Kasuwan Mashigin Taiwan

Ta ce tuni Sin ta sanar da cewa shugabanta Xi Jinping zai ziyarci Amurka bisa gayyatar da aka yi masa, tana mai cewa, shugabannin biyu za su yi tattaunawa mai zurfi kan muhimman batutuwan da suka shafi kyautata dangantakar kasashensu da ma manyan batutuwan dake da alaka da zaman lafiya da ci gaban duniya.

Ta ce a huldarta da Amurka, kasar Sin ta kasance mai bin ka’idojin mutunta juna da dangantakar moriyar juna da shugabanta ya gabatar. Kuma takara tsakanin kasashe ba ta dace da yanayin da ake ciki ba, haka kuma ba za ta warware matsalolin Amurka ko kalubalen duniya ba.

Da aka tabo batun Taiwan, Mao Ning ta ce wannan batu ne na cikin gidan Sin da al’ummarta ne kadai za su iya warwarewa. Kuma yayin ganawar da suka yi a tsibirin Bali, gwamnatin Amurka ta bayyana karara cewa ba ta goyon bayan ‘yancin kan yankin, don haka ya kamata ta kiyaye tare da bin manufar kasar Sin daya tak a duniya, kana ta yi adawa da ayyukan dake neman ‘yancin kan Taiwan.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Dangane da batun Tekun Kudancin Sin kuwa, kakakin ta ce a shirye Sin take ta warware matsalar tare da kasashe masu ruwa da tsaki ta hanyar tattaunawa da tuntubar juna. Haka kuma a shirye take ta kare cikakken ‘yanci da yankunanta.

Har ila yau, Mao Ning ta bayyana cewa, duniya na sa ido sosai kan rikicin Palasdinu da Isra’ila, kuma har kullum, Sin na goyon bayan adalci, kana tana tuntubar dukkan bangarori, kuma burinta shi ne ganin an dakatar da rikicin tare da kare fararen hula.

Ta ce Sin na fatan Amurka za ta dauki matsayar da ta dace da taka rawar gani wajen ganin an dakatar da bude wuta nan ba da jimawa ba. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 5, Sun Kwato Makamai A Kaduna

Next Post

Yadda Ma’aikatan MDD A Nijeriya Suka Girmama Takwarorinsa Da Aka Kashe A Gaza

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

8 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

9 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

10 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

11 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

13 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Yadda Ma’aikatan MDD A Nijeriya Suka Girmama Takwarorinsa Da Aka Kashe A Gaza

Yadda Ma’aikatan MDD A Nijeriya Suka Girmama Takwarorinsa Da Aka Kashe A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.