• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Kyakkyawan Fata Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Wannan Karo

by CGTN Hausa
2 years ago
sin

Ga duk mai bibiyar muhimman harkokin dake gudana a ’yan kwanakin nan, ba zai gaza lura da yadda hankula suka karkata ga ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping yake yi a kasar Amurka ba, duba da yadda wannan ziyara ta yi matukar jan hankulan sassan kasa da kasa, inda tuni shugaba Xi ya gana kai tsaye tare da takwaransa na Amurka, kuma mai masaukinsa Joe Biden, a katafaren gidan alfarman nan na Filoli dake birnin San Francisco, ganawar ido da ido da ta kasance ta farko tsakanin shugabannin biyu, tun bayan haduwarsu a tsibirin Bali na  Indonesia a shekarar bara.

Bayan tattaunawa tsakanin shugabannin biyu game da muhimman batutuwa, da musayar ra’ayoyi kan abubuwan dake matukar jan hankulan kasashensu, musamman wadanda suka jibanci yadda za a farfado, da kara kyautata dangantakar Sin da Amurka, da ma batutuwan dake shafar zaman lafiya da ci gaban duniya, da dama daga masharhanta na ganin ganawar ta yi armashi.

  • Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Zaben Gwamnan Zamfara A Matsayin Bai Kammala Ba
  • Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

Har ma wasu masu fashin baki na ganin shugabannin kasashen biyu, suna sane da cewa duniya ta zuba ido domin ganin rawar da za su taka a wannan gaba da duniya ke fuskantar manya manyan kalubale a mataki na kasa da kasa da ma na shiyyoyi.

Duniya ta yi imanin cewa, alakar Sin da Amurka tana da muhimmancin koli, kuma kyautatarta zai ingiza ci gaban duniya, don haka ya dace a yi duk mai yiwuwa wajen inganta ta.

Masu fashin baki sun dade da amincewa, cewa idan har Sin da Amurka suka juyawa juna baya, hakan zai haifar da mummunan sakamako ga duniya, baya ga illar da hakan zai yi a gare su, don haka ba hanya ce mai bullewa ba. Kaza lika ba abu ne mai yiwuwa daya daga cikin manyan kasashen biyu ta yi yunkurin sauya dayar ba, kuma rura wutar rikici, ko fito na fito tsakanin su ba zai haifarwa kowa da mai ido ba.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

Tabbas, mummunar takara tsakanin manyan kasashe masu fada a ji ba ta dace da muradun wannan zamani ba, kuma hakan ba zai warware tarin kalubale da Sin da Amurka ke fuskanta, da ma matsalolin sauran sassan duniya ba. Don haka fatan dukkanin sassan kasa da kasa a wannan gaba da wadannan shugabanni na manyan kasashen duniya ke tattaunawa, shi ne su kai ga cimma nasarar dinke baraka, su rungumi juna, tare da amincewa cewa nasarorin da suke cimmawa, damammaki ne na bunkasar juna.

Ko shakka babu, muddin kasashen Sin da Amurka sun martaba juna, sun rungumi hadin gwiwar cimma moriya tare cikin lumana, bangarorin biyu za su cimma nasarar shawo kan sabanin dake tsakaninsu, tare da zakulo hanya madaidaiciya ta zaman jituwa mai alfanu. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki
Daga Birnin Sin

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Next Post
Akwai Kyakkyawan Fata Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Wannan Karo

Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Ba Da Tallafin Kudi Don Inganta Hadin Gwiwar Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.