ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Kyakkyawan Fata Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Wannan Karo

by CGTN Hausa
3 years ago
sin

Ga duk mai bibiyar muhimman harkokin dake gudana a ’yan kwanakin nan, ba zai gaza lura da yadda hankula suka karkata ga ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping yake yi a kasar Amurka ba, duba da yadda wannan ziyara ta yi matukar jan hankulan sassan kasa da kasa, inda tuni shugaba Xi ya gana kai tsaye tare da takwaransa na Amurka, kuma mai masaukinsa Joe Biden, a katafaren gidan alfarman nan na Filoli dake birnin San Francisco, ganawar ido da ido da ta kasance ta farko tsakanin shugabannin biyu, tun bayan haduwarsu a tsibirin Bali na  Indonesia a shekarar bara.

Bayan tattaunawa tsakanin shugabannin biyu game da muhimman batutuwa, da musayar ra’ayoyi kan abubuwan dake matukar jan hankulan kasashensu, musamman wadanda suka jibanci yadda za a farfado, da kara kyautata dangantakar Sin da Amurka, da ma batutuwan dake shafar zaman lafiya da ci gaban duniya, da dama daga masharhanta na ganin ganawar ta yi armashi.

  • Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Zaben Gwamnan Zamfara A Matsayin Bai Kammala Ba
  • Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

Har ma wasu masu fashin baki na ganin shugabannin kasashen biyu, suna sane da cewa duniya ta zuba ido domin ganin rawar da za su taka a wannan gaba da duniya ke fuskantar manya manyan kalubale a mataki na kasa da kasa da ma na shiyyoyi.

ADVERTISEMENT

Duniya ta yi imanin cewa, alakar Sin da Amurka tana da muhimmancin koli, kuma kyautatarta zai ingiza ci gaban duniya, don haka ya dace a yi duk mai yiwuwa wajen inganta ta.

Masu fashin baki sun dade da amincewa, cewa idan har Sin da Amurka suka juyawa juna baya, hakan zai haifar da mummunan sakamako ga duniya, baya ga illar da hakan zai yi a gare su, don haka ba hanya ce mai bullewa ba. Kaza lika ba abu ne mai yiwuwa daya daga cikin manyan kasashen biyu ta yi yunkurin sauya dayar ba, kuma rura wutar rikici, ko fito na fito tsakanin su ba zai haifarwa kowa da mai ido ba.

LABARAI MASU NASABA

Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

Tabbas, mummunar takara tsakanin manyan kasashe masu fada a ji ba ta dace da muradun wannan zamani ba, kuma hakan ba zai warware tarin kalubale da Sin da Amurka ke fuskanta, da ma matsalolin sauran sassan duniya ba. Don haka fatan dukkanin sassan kasa da kasa a wannan gaba da wadannan shugabanni na manyan kasashen duniya ke tattaunawa, shi ne su kai ga cimma nasarar dinke baraka, su rungumi juna, tare da amincewa cewa nasarorin da suke cimmawa, damammaki ne na bunkasar juna.

Ko shakka babu, muddin kasashen Sin da Amurka sun martaba juna, sun rungumi hadin gwiwar cimma moriya tare cikin lumana, bangarorin biyu za su cimma nasarar shawo kan sabanin dake tsakaninsu, tare da zakulo hanya madaidaiciya ta zaman jituwa mai alfanu. (Saminu Alhassan)

sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Tattauna Da Shugaban Slovak A Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wang Jian: Muna Fatan Mutanen Afirka Za Su Kara Cin Gajiyar Fasahar AI

MASU ALAKA

Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

July 28, 2026
Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

July 28, 2026
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Slovak A Beijing
Daga Birnin Sin

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Slovak A Beijing

July 28, 2026
Next Post
Akwai Kyakkyawan Fata Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Wannan Karo

Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Ba Da Tallafin Kudi Don Inganta Hadin Gwiwar Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Babu Wani Ɗan Nijeriya Da Zai Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

July 28, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Soke Umarnin Cire Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu Huɗu

July 28, 2026
Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

July 28, 2026
Ruwa

2027: Gwamnan Kaduna Ya Sanar Da Sabon Mataimakinsa A Zaɓen Gwamna

July 28, 2026
Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

July 28, 2026
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Slovak A Beijing

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Slovak A Beijing

July 28, 2026
Rimin-gado Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Batun Yi Wa ‘Yan Daba Alfarma A Kano

Rimin-gado Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Batun Yi Wa ‘Yan Daba Alfarma A Kano

July 28, 2026
Wang Jian: Muna Fatan Mutanen Afirka Za Su Kara Cin Gajiyar Fasahar AI

Wang Jian: Muna Fatan Mutanen Afirka Za Su Kara Cin Gajiyar Fasahar AI

July 28, 2026
An Kaddamar Da Shirye-Shiryen Hadin Gwiwar Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka A Habasha

An Kaddamar Da Shirye-Shiryen Hadin Gwiwar Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka A Habasha

July 28, 2026
Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole

Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole

July 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.