ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Kyakkyawan Fata Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Wannan Karo

by CGTN Hausa
3 years ago
sin

Ga duk mai bibiyar muhimman harkokin dake gudana a ’yan kwanakin nan, ba zai gaza lura da yadda hankula suka karkata ga ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping yake yi a kasar Amurka ba, duba da yadda wannan ziyara ta yi matukar jan hankulan sassan kasa da kasa, inda tuni shugaba Xi ya gana kai tsaye tare da takwaransa na Amurka, kuma mai masaukinsa Joe Biden, a katafaren gidan alfarman nan na Filoli dake birnin San Francisco, ganawar ido da ido da ta kasance ta farko tsakanin shugabannin biyu, tun bayan haduwarsu a tsibirin Bali na  Indonesia a shekarar bara.

Bayan tattaunawa tsakanin shugabannin biyu game da muhimman batutuwa, da musayar ra’ayoyi kan abubuwan dake matukar jan hankulan kasashensu, musamman wadanda suka jibanci yadda za a farfado, da kara kyautata dangantakar Sin da Amurka, da ma batutuwan dake shafar zaman lafiya da ci gaban duniya, da dama daga masharhanta na ganin ganawar ta yi armashi.

  • Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Zaben Gwamnan Zamfara A Matsayin Bai Kammala Ba
  • Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

Har ma wasu masu fashin baki na ganin shugabannin kasashen biyu, suna sane da cewa duniya ta zuba ido domin ganin rawar da za su taka a wannan gaba da duniya ke fuskantar manya manyan kalubale a mataki na kasa da kasa da ma na shiyyoyi.

ADVERTISEMENT

Duniya ta yi imanin cewa, alakar Sin da Amurka tana da muhimmancin koli, kuma kyautatarta zai ingiza ci gaban duniya, don haka ya dace a yi duk mai yiwuwa wajen inganta ta.

Masu fashin baki sun dade da amincewa, cewa idan har Sin da Amurka suka juyawa juna baya, hakan zai haifar da mummunan sakamako ga duniya, baya ga illar da hakan zai yi a gare su, don haka ba hanya ce mai bullewa ba. Kaza lika ba abu ne mai yiwuwa daya daga cikin manyan kasashen biyu ta yi yunkurin sauya dayar ba, kuma rura wutar rikici, ko fito na fito tsakanin su ba zai haifarwa kowa da mai ido ba.

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Tabbas, mummunar takara tsakanin manyan kasashe masu fada a ji ba ta dace da muradun wannan zamani ba, kuma hakan ba zai warware tarin kalubale da Sin da Amurka ke fuskanta, da ma matsalolin sauran sassan duniya ba. Don haka fatan dukkanin sassan kasa da kasa a wannan gaba da wadannan shugabanni na manyan kasashen duniya ke tattaunawa, shi ne su kai ga cimma nasarar dinke baraka, su rungumi juna, tare da amincewa cewa nasarorin da suke cimmawa, damammaki ne na bunkasar juna.

Ko shakka babu, muddin kasashen Sin da Amurka sun martaba juna, sun rungumi hadin gwiwar cimma moriya tare cikin lumana, bangarorin biyu za su cimma nasarar shawo kan sabanin dake tsakaninsu, tare da zakulo hanya madaidaiciya ta zaman jituwa mai alfanu. (Saminu Alhassan)

sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
Akwai Kyakkyawan Fata Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Wannan Karo

Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Ba Da Tallafin Kudi Don Inganta Hadin Gwiwar Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.