• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Makoma Mai Haske Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

byCMG Hausa
3 years ago
Sin

A baya bayan nan, hukumar lafiya ta duniya WHO ta bayyana raguwar adadin masu harbuwa da cutar COVID-19 a nahiyar Afirka da kaso mai yawa, tun daga tsakiyar watan Afirilun da ya gabata, raguwar da a cewar hukumar ita ce mafi tsawo da aka samu a nahiyar tun bullar wannan annoba kawo yanzu.

Ko shakka babu wannan labari ne mai faranta rai ga duniya baki daya. To sai dai kuma, wani jan aiki dake gaban kasashen nahiyar ta Afirka a yanzu shi ne lalubo hanyoyin shawo kan mummunan tasirin da wannan annoba ta haifar musamman ta fuskar tattalin arzikin Afirka.

  • Sin Tana Adawa Da Dokar Hana Kayayyakin Da Suka Shafi Jihar Xinjiang Shiga Amurka

Hakan ne ma ya sa masharhanta da dama ke ganin ya zama wajibi kasashen Afirka su karfafa hadin gwiwarsu da kasar Sin, karkashin muhimman manufofin hadin kai da sassan biyu suka jima da amincewa da su, wadanda suka hada da manufofin da aka tsara karkashin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, da ayyukan samar da moriya dake kunshe cikin shawarar nan ta ziri daya da hanya daya da sauran su.

A halin da ake ciki, kasar Sin ce babbar abokiyar huldar nahiyar Afirka ta fuskar kasuwanci cikin sama da shekaru 10, kuma kasar da kamfanoninta ke kara zuba jari mai yawan gaske a nahiyar, wanda adadinsa ya karu a watanni 7 na farkon shekarar 2021 zuwa dalar Amurka biliyan 2.07.

A bangaren nahiyar Afirka, masana na cewa, nahiya ce dake da tarin albarkatun kasa, da maadanai masu daraja, da man fetur da iskar gas, da damar samar da makamashi daga hasken rana, da fadin kasar noma mai yalwa, da tarin alumma dake cikin shekarun kwadago.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Sai dai kuma kalubalen rashin masanaantu, da kamfar makamashi, ya zamowa nahiyar kadangaren bakin tulu, ta yadda kasashen nahiyar ba sa samun damar cin gajiyar da ta dace daga albarkatunta. Hakan ya sa kasashen Afirka da dama kasancewa cikin jerin kasashe mafiya fama da talauci a duniya.

Duk da wadannan tarin kalubale, akwai makoma mai haske ga kasashen na Afirka, muddin sun ci gaba da nacewa aiwatar da kudurorin dake kunshe cikin ajandojin wanzar da ci gaban su, tare da babbar manufar nan ta raya hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ta nan da shekarar 2035, ko China-Africa Cooperation Vision 2035 a Turance, da ma shirin dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da Afirka na Dakar, mai kunshe da tsarin ayyuka da za a aiwatar tsakanin shekarar nan ta 2022 zuwa 2024.

Dukkanin wadannan kudurori ne da ke kunshe cikin babbar manufar nan ta shawarar ziri daya da hanya daya da kasar Sin ta gabatarwa duniya, wadda ko shakka babu, ci gaba da aiwatar da ita zai haifarwa kasashen na Afirka tarin alfanu nan da shekaru masu zuwa. (Saminu Hassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Yadda Wani Lauya Ya Tarwatsa Dakin Shari’a Da Shigar Matsubbata

Yadda Wani Lauya Ya Tarwatsa Dakin Shari'a Da Shigar Matsubbata

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version