ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Makoma Mai Haske Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

by CMG Hausa
4 years ago
Sin

A baya bayan nan, hukumar lafiya ta duniya WHO ta bayyana raguwar adadin masu harbuwa da cutar COVID-19 a nahiyar Afirka da kaso mai yawa, tun daga tsakiyar watan Afirilun da ya gabata, raguwar da a cewar hukumar ita ce mafi tsawo da aka samu a nahiyar tun bullar wannan annoba kawo yanzu.

Ko shakka babu wannan labari ne mai faranta rai ga duniya baki daya. To sai dai kuma, wani jan aiki dake gaban kasashen nahiyar ta Afirka a yanzu shi ne lalubo hanyoyin shawo kan mummunan tasirin da wannan annoba ta haifar musamman ta fuskar tattalin arzikin Afirka.

  • Sin Tana Adawa Da Dokar Hana Kayayyakin Da Suka Shafi Jihar Xinjiang Shiga Amurka

Hakan ne ma ya sa masharhanta da dama ke ganin ya zama wajibi kasashen Afirka su karfafa hadin gwiwarsu da kasar Sin, karkashin muhimman manufofin hadin kai da sassan biyu suka jima da amincewa da su, wadanda suka hada da manufofin da aka tsara karkashin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, da ayyukan samar da moriya dake kunshe cikin shawarar nan ta ziri daya da hanya daya da sauran su.

ADVERTISEMENT

A halin da ake ciki, kasar Sin ce babbar abokiyar huldar nahiyar Afirka ta fuskar kasuwanci cikin sama da shekaru 10, kuma kasar da kamfanoninta ke kara zuba jari mai yawan gaske a nahiyar, wanda adadinsa ya karu a watanni 7 na farkon shekarar 2021 zuwa dalar Amurka biliyan 2.07.

A bangaren nahiyar Afirka, masana na cewa, nahiya ce dake da tarin albarkatun kasa, da maadanai masu daraja, da man fetur da iskar gas, da damar samar da makamashi daga hasken rana, da fadin kasar noma mai yalwa, da tarin alumma dake cikin shekarun kwadago.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Sai dai kuma kalubalen rashin masanaantu, da kamfar makamashi, ya zamowa nahiyar kadangaren bakin tulu, ta yadda kasashen nahiyar ba sa samun damar cin gajiyar da ta dace daga albarkatunta. Hakan ya sa kasashen Afirka da dama kasancewa cikin jerin kasashe mafiya fama da talauci a duniya.

Duk da wadannan tarin kalubale, akwai makoma mai haske ga kasashen na Afirka, muddin sun ci gaba da nacewa aiwatar da kudurorin dake kunshe cikin ajandojin wanzar da ci gaban su, tare da babbar manufar nan ta raya hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ta nan da shekarar 2035, ko China-Africa Cooperation Vision 2035 a Turance, da ma shirin dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da Afirka na Dakar, mai kunshe da tsarin ayyuka da za a aiwatar tsakanin shekarar nan ta 2022 zuwa 2024.

Dukkanin wadannan kudurori ne da ke kunshe cikin babbar manufar nan ta shawarar ziri daya da hanya daya da kasar Sin ta gabatarwa duniya, wadda ko shakka babu, ci gaba da aiwatar da ita zai haifarwa kasashen na Afirka tarin alfanu nan da shekaru masu zuwa. (Saminu Hassan)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Yadda Wani Lauya Ya Tarwatsa Dakin Shari’a Da Shigar Matsubbata

Yadda Wani Lauya Ya Tarwatsa Dakin Shari'a Da Shigar Matsubbata

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.