• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’adar Tashe A Kasar Hausa

by Ishaq Idris Gulbi
1 year ago
in Al'adu
0
Al’adar Tashe A Kasar Hausa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

(Na taba gabatar da wannan kasida a jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo ta ranar litinin 25 ga watan Janairun shekarar 1999).

Ma’anar Tashe

Kalmar TASHE ana kyautata zaton ta yo asali ne daga Kalmar TASHI   ko TASA. Wato kamar ka tashi mutum daga barci ko daga zaune ko kishingide. wasan Tashe kuwa na nufin ta da/tayar da mutum cikin raha da nishadi da kayatarwa.

Tashe wasa ne da ya yi suna kuma ya shahara a kasar Hausa. Ana yinsa ne a lokacin da wata Azumi ya kai goma. Wasa ne da bai bar kowa ba domin kuwa ba babba babu yaro, ba mace babu namiji kowa yakan yi irin nasa daidai gwargwado.

Tarihin Tashe

Labarai Masu Nasaba

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

GORON JUMA’A 20-06-2025

Wasu sun ce Tashe ya shigo kasar Hausa ne bayan zuwan addinin musulunci a karni na goma sha daya idan aka lura da fasalinsa da kyau. Akan yi Tashe da daddare a wadansu wuraren ma har da rana ana yi ko da safe. Akwai Tashe iri-iri a kalla iri dari. Wadansu masu ban dariya, wadansu su ilimantar tare da nishadantarwa. Wasu kuwa cike da abubuwan tausayi da ban al’ajabi ko tarihi. Wadansu maza zar ke yinsu, wadansu kuwa ‘yan mata. A wasu Tashen akan samu haduwar ‘yan maza da ‘yan mata, kuma kamar yadda yara ke wasan Tashe haka nan manya ma ke yi.

Misalan Tashe

Misalin wasan Tashe na ‘yan maza zar shi ne Tashen Macukule, inda shi jagoran Tashen zai sanya wata irin fuska ko ya shafe fuskarsa da bula ko toka, sauran ‘yan wasan kuma suna biye da shi yana sa waka suna amsa masa kamar haka:

Jagora:  Kan kare da dadi.

‘Yan amshi:  Macukule

Jagora:  Majina Kitse ce

‘Yan amshi:  Macukule

Jagora:  Kan agwagwa taushe

‘Yan amshi:  Macukule

Wannan Tashe na Macukule bayan kasancewarsa na maza zar ne, har ila yau yana taimaka wa mutum sanin irin wasan (barkwanci) da ke tsakanin Hausa da Gwari/Gbagi, domin kuwa irin wannan wasa ko yi wa juna barkwanci, ba sabon abu ba ne a tsakanin Hausa da Fulani, Fulani da Barebari, Hausawa da Inyamurai, Kanawa da Zage-zagi da dai sauran kabilu da aka taba samun wata dangantaka a tsakaninsu da Hausawa.

Sauran Tashen da maza kadai ke yi sun hada da:

  1. Ka yi rawa kai malam ka yi rawa
  2. Jatau mai magani
  3. Mai kiriniya
  4. Tsoho da gemu da dai sauransu.

Na ‘yan mata zalla kuwa sun hada da:-

  1. Mai ciki
  2. Iya duba cikina
  3. Hajiyar kauye
  4. Mairama ga Daudu

‘Yan Tashe kan bi gida-gida, ko kasuwanni ko kauyuka da tituna ko birane domin yin Tashen, kuma duk inda suka yi Tashen akan yi masu dan abin hasafi. Akan ba su gero ko dawa ko kudI, in kuma kasuwa suka shiga su samo kayan miya da sauran abubuwa da ke wannan kasuwa.

Muhimmancin Tashe

Tashe yana da muhimmanci kwarai da gaske da in muka ce za mu tsaya lissafa muhimmancinsa sai mun kusan shekara ba mu kamala ba. Baya ga irin nishadantar da jama’a da wasan Tashe ke yi, har ila yau Tashe tamkar wata taska ce da ke makare da al’adar Hausawa domin kuwa da zaran lokacin ya kewayo sai ya sa tsofaffi sun tuna lokacin da suke yara. In ba yanzu da dinbin bakin abubuwa suka samu gindin zama a cikin Tashen ba, in ka kira Tashe da sunan MADUBIN HOTON ADABIN HAUSA  ba karya ka yi ba.

Har ila yau wasan Tashe na taimaka wa yaro wajen kara fahimtar al’adarsa da al’umarsa wadanda za su yi tasiri wajen tarbiyyantar da shi a matsayin yara manyan gobe, da kuma kara masa basirar yadda zai yi amfani su ta hanyoyin da suka dace.

Hasali ma Tashe na taimaka wa sauran al’uma da ke makwabtaka da Hausawa kamar su Inyamurai da Yarbawa da sauran kabilu su fahimci Hausawa da zamantakewarsu, da addininsu da siyasarsu har su yaba.

A zamanin da, Tashe yana daya daga cikin kwararan hanyoyi tattaro yara, da dan manomi da na masaki, da na maharbi da na mahauci da sauransu zuwa wuri guda, su shirya wasannin Tashe iri-iri har na tsawon kwana ashirin. Har in suna yawon Tashen akan gamu da wasu ‘yan Tashen da kan ce ‘Kura ta ci kura’ Ku kuma ku mayar da martini ku ce ‘Ta ci in ta samu’

Kuma ana amfani da tashe wajen karfafa wa al’umar Musulmi kwarin gwiwar kara dukufa ga bauta wa Ubangiji kamar yadda yake a cikin tashen nan da ake cewa:-

Jagora: A sha ruwa-ruwa a sha ruwa ai sallah,

‘Yan amshi: A sha ruwa

Jagora: masu gidan nan barci kuke ko sallah,

‘Yanamshi: A sha ruwa

Jagora :In barci ne ku tashi domin Allah,

‘Yan amshi: A sha ruwa

Jagora: In sallah ce ku yi ta domin Allah.

Matsalolin Tashe a Yau

To abin ban takaici shi ne duk da wadannan dinbin muhimmancin da Tashe yake da su, yana ta kara samun fuskantar kisan gilla daga ko ta wane bangare. Muhimmi daga cikin irin matsalolin da suka dabaibaye Tashe shi ne watsi da Hausawa suka yi da al’adar ta Tashe, ballantana har su yi tunanin habaka shi.

Kusan babu wani kokarid a manyan malaman Hausa da ke tsibe a manyan makarantunmu na ilimi. Su kuma yara a yanzu sai kwallon kafa da kallon fina-finai da sauran karance-karance da suka saba wa dabi’arsu.

Bugu da kari ga satar yara da ake ta fama da ita a yanzu da ya sa kowa idan yamma ta yi sai ya garkame ‘ya’yansa a gida ko leke babu.

Sannan yanayi kan canza domin a wasu lokutan za ka ga Tashe ya fado a lokaci na hunturu ko damina da yaran ko dai dari ya hana su fita, ko in sun fita ruwan sama ya musu duka. Ko sun nace sun yi tashen, gidajen da za su shiga yin Tashen za su tarar kowa ya kulle kofarsa babu kowa a tsakar gida.

Su kuma gidajen rediyon da ke Arewacin kasarnan musamman gidan Rediyon Tarayya na Kaduna suna kokarin sanya wasannin Tashen da watan Azumi, sai dai su ma sun rage himma da lokaci saboda kudi da aka dage ana nema, ake ta fafutukar neman wadanda za su dau nauyin sanya Tashen. Wata kila shi ya sanya gidan Rediyon Tarayya na Kaduna ya rage lokutan sanya Tashen. In kuwa haka ne, to wannan babbar kalubale ce ga sassan nazarin harshen Hausa da muke das u a jami’o’inmu. In wani bai iya daukar wannan nauyi, su hakkinsu ne su dauka kamar yadda sassan binciken aikin noma na jami’o’I ke yi a su talabijin da rediyo.

Wani abin kuma da ke barazana ga Tashe shi ne tabarbarewar da tattalin arzikin kasarnan ya yi da jefaal’umarta cikin halin kaka-ni-kayi komai ya tsauwala gas hi ba kudi. Gidaje da yawa sai ka tarar an yi kwana da kwanaki ba a dora sanwa ba. To ina ga wadanda suka zo Tashe? A da bayan an kare kwanakin Tashe sai ka tarar yara sun tara hatsi kusan buhu ko buhunhuna. Amma a yanzu ko mudu ba sa hadawa. Haka zalika za su kare bas u sami ko kwabo ba, wasu wuraren ma idan sun je ko dai a kore su, ko a mayar da su marasa aikin yi, ko kauyawa.

Mafita

Ina mafita? Tunda mun san irin matsalolin da ke addabar Tashe, ya zama wajibi akan duk wanda ya san yana da hakki a kai musamman Hausawa da sauran cibiyoyin ilmi da ke da nasaba da harshen Hausa da sauran kungiyoyin Hausa, su mike tsaye su yi wani abu akai, in ba haka ba su wayi gari wata rana su tarar Tashe ya sheka lahira sai labara.

IS’HAK IDRIS GUIBI, Kaduna, ana iya samun sa ta:

[email protected]


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma

Next Post

Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

Related

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya
Goron Juma'a

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2 weeks ago
GORON JUMA’A 16/05/2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 20-06-2025

3 weeks ago
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana
Al'adu

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

1 month ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 30-03-2025

1 month ago
GORON JUMA’A 16/05/2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 16/05/2025

2 months ago
GORON JUMA’A
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 28-03-2025

3 months ago
Next Post
Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

July 9, 2025
Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

July 9, 2025
Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

July 9, 2025
Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

July 9, 2025
Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

July 9, 2025
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.