ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

by Sulaiman Bala Idris and Sulaiman
10 months ago
Dauda Lawal

Ba ni da kokwanto akan cewa, Dauda Lawal na ɗaya daga cikin gwamnonin da suka fi kowa kwarjini a Nijeriya. Amma abu ɗaya da nake yawan samun ƙalubalen bayyana wa mutane shi ne shekarun sa.

 

Mutane su kan yi ihun ‘kai!’ wasu kuma su kan kalli idona cikin wasa da dariya su ƙaryata ni. Duk saboda na bayar da sahihin bayanin da na tabbata ɗari bisa ɗari akan cewa Dauda Lawal zai cika 60 a ranar 2 ga Satumba, 2025 (wato yau).

ADVERTISEMENT

 

Wani lokaci, na kan gaji da bayyani. Ko da a ƙarshe sun yarda da shekarun sa, wasu mutane suna cusa musu shakku daga baya. Wasu suna nuna cewa ya bayyana a matsayin matashi kuma yana gyara kan sa ne saboda yana da dukiya.

LABARAI MASU NASABA

Goron Juma’a

GORON JUMA’A 22-05-2026

 

Kun tuna jita-jitar ake yaɗawa game wai arzikin sa ya kai Naira Tiriliyan 9? Kuma Mutane da yawa sun gaskata.

 

A matsayin sa na gwamnan jihar Zamfara, ina da abubuwa da yawa da zan iya cewa game da Dauda Lawal, musamman da yake ina cikin makusantan sa, mai yin aiki kafaɗa da kafaɗa da shi a matsayin kakakin sa sama da shekaru biyu.

 

A shekarun baya na yi rubuce-rubuce da dama a kan Dauda Lawal, ma’aikacin banki kuma mai taimakon al’umma.

 

Amma, yayin da ya cika shekara 60 a yau, zan so in fitar da wasu ’yan muhimman abubuwa da Dauda Lawal ya yi a matsayin gwamna, wanda ke mayar da Jihar Zamfara daga kufai da aka manta da ita zuwa babban birnin.

 

Dukkan abubuwan da mutane ke faɗi game da shi natsuwa, kamun kia, da tsabta daidai ne. Ya canja ɗabi’ar ma’aikata, musamman waɗanda ke gidan gwamnatin Zamfara, waɗanda ke aiki a kan kujerar mulki. Salon rayuwarsu ta canja, ba kamar da ba.

 

Gusau, babban birnin jihar, an gyara ta a matsayin cibiyar birane, kamar yadda ya kamata. An shimfiɗa titi tare da saka fitilu masu haske a ko’ina. Gusau, wacce ba ta da fitilun warware cunkoson ababen hawa a 2023 kafin zabe, yanzu haka tana da fitilun a duk faɗin birnin. Garin ya ƙawatu saboda a hankali ɗabi’un mutane yana canjawa.

 

A matsayina na mai fafutukar nuna ma’amala ta ƙwarai, ɗaya daga cikin manyan makarantun tunani na zamantakewar al’umma, na lura da yadda ƙa’idar ‘Kallo Ta Cikin Gilashi’ ta Charles Horton Cooley ke aiwatarwa a tafiyar Gwamna Dauda Lawal a Zamfara. Za ku iya cewa ta ya.

 

Kallo Ta Cikin Gilashi ra’ayi ne da ke bayyana yadda mutane ke yin tunanin kansu dangane da yadda suke tunanin wasu na fahimtar su. Ta hanyar hulɗar zamantakewa, mutane suna amfani da maganganun wasu a matsayin “madubi” don tantance ƙimarsu, ɗabi’a, da halayensu.

 

A da, abin da mutane ke gani game da Zamfara idan suka kalli madubi, shi ne halin da ake ciki na ƙaƙani-ka-yi, jihar da ’yan bindiga da talauci suka kusa kawar da ita. Ita ce ƙarshe baya da fannin ilimi da kiwon lafiya. Dauda Lawal, masanin kimiyyar siyasa, ya canja wannan labari ta hanyar haɗa ƙa’idojin zamantakewa na aiki da ma’amala mai kyau.

 

Jihar Zamfara da mutane ke gani a madubi a yanzu, jiha ce da ke takara a matsayin jiha mafi inganci a fannin tattalin arzikin cikin gida, ilimi, cibiyoyi masu tasowa, kiwon lafiya, da sauransu.

 

Aikin ceto na Gwamna Dauda Lawal ya bayyana a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar Zamfara, ba wai a Gusau, babban birnin jihar kaɗai ba.

 

Waɗannan manyan ayyuka sun shafi sassa daban-daban, waɗanda suka haɗa da kiwon lafiya, ilimi, ababen more rayuwa, da sauran muhimman wurare masu.

 

Gwamna Lawal ya mayar da Babban Asibitin Anka zuwa wani katafaren asibiti na zamani mai ɗauke da na’urorin kiwon lafiya na zamani a ƙaramar hukumar Anka. An yi wa asibitin gyaran ciki da waje.

 

Gwamnatinsa ta kafa makarantar Tsangaya ta zamani a Ƙaramar Hukumar Gummi, makarantar da aka tsara don shigar da Almajirai cikin tsarin ilimi na zamani.

 

A ƙaramar hukumar Bakura, Gwamna Lawal ya gyara Kwalejin Kimiyyar Aikin Gona tare da samar mata da kayan aiki, inda ya samar da damarmaki ga matasa don bunƙasa sana’ar su ta noma — ƙashin bayan tattalin arzikin Zamfara.

 

A Ƙaramar Hukumar Bukkuyum, ya ɗaukaka darajar PHC Nasarawa Burkullu zuwa babban asibitin zamani da na’urori na zamani domin amfanin al’ummar yankin. Bugu da ƙari, ya bayar da kwangilar gina titunan garin domin haɗa dukkan garuruwan da ke cikin ƙaramar hukumar.

 

Gwamna Dauda Lawal ya gyara babban asibitin da ke Ƙaramar Hukumar Maru tare da cikakken kayan aiki. Asibitin, wanda a baya ya yi fata-fata, yanzu an gyara shi yadda ya kamata.

 

A Ƙaramar Hukumar Talatar Mafara, Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da aikin gina sabon babban asibiti, domin a halin yanzu asibitin ya lalace. Sauran ayyukan a Talata Mafara sun haɗa da gyare-gyare a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Zamfara.

 

A Ƙaramar Hukumar Maradun, Gwamna Lawal ya inganta tare da gyara babban asibitin Maradun, inda ya mayar da shi Cibiyar Kula da Lafiya ta Zamani mai ɗauke da duk wasu kayayyakin jinya na zamani. Ya kuma gyara babban asibitin Maru tare da samar da na’urori na zamani.

 

Hakazalika, a ƙaramar hukumar Kauran Namoda, Gwamna Lawal ya gyara babban asibitin Kaura Namoda tare da samar da kayan aiki, ya gina makarantar Tsangaya na zamani, ya kafa cibiyar koyar da sana’o’i da ta dace domin samar da ayyukan yi ga matasa, da kuma gina ƙarin gidajen kwana a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kauran Namoda.

 

A Ƙaramar Hukumar Shinkafi, Gwamna Lawal ya amince da sake gina babban asibitin Shinkafi da kuma aikin sake gina makarantar Attahiru Bafarawa.

 

A Ƙaramar Hukumar Tsafe, Gwamna Dauda Lawal ya gyara babban asibitin Tsafe tare da samar da kayan aiki, ya kuma gudanar da gyaran gaba ɗaya na Makarantar Koyon Fasaha ta Tsafe, ya sake gina babbar tashar mota ta zamani ta Tsafe, da sake gina babbar kasuwa.

 

A Ƙaramar Hukumar Bungudu, Gwamna Lawal yana gina titin mahaɗa na Furfuri, titin Rawayya, aikin gyaran makarantar da aka amince da shi gaba ɗaya, da kuma aikin gyara da kayan aiki na makarantar sakandaren Ɗan Gwaggo.

 

Ina da abubuwa da yawa da zan faɗa, musamman game da dangantakar mutane da gwamna na. Na yi alƙawari zan yi shi a hankali, ba a lokaci guda ba. Yau rana ce da za a yi bikin mai nasara. Alhamdu lillah, barka da cika shekaru 60 ga mutum mai kyakkyawar zuciya.

 

Barka da Ranar Haihuwa, Oga!

 

Sulaiman shi ne kakakin gwamnan jihar Zamfara.

 

Fassarar MAHDI MUSA MUHAMMAD

Dauda Lawal
Sulaiman Bala Idris
+ posts Bio
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    ‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Hayaniya ‘Yar Facebook!
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Mummunan Zato
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Me Ake Nufi Da Ado? 
Dauda Lawal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Sulaiman
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • Sulaiman
    Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci
  • Sulaiman
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

MASU ALAKA

GORON JUMA’A 17-04-2026
Goron Juma'a

Goron Juma’a

June 5, 2026
GORON JUMA’A 01-07-2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 22-05-2026

May 22, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
Labarai

Ku Kula Da Kyawawan Ɗabi’u, Su Ne Waɗanda Annabi SAW Ya Kira Duk Halitta A Kansu

April 17, 2026
Next Post
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.