• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ajabi: Yadda Wani Maniyyaci Ya Fara Aikin Hajjinsa A Sansanin Alhazai Na Kano Bayan Rasa Kujerarsa

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Al'ajabi
0
Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani abu mai kama da wasan kwaikwayo da ya faru a Kano ranar Alhamis, inda wani Maniyyaci wanda bai samu shiga cikin jirgin karshe zuwa Saudiyya ba, ya kaddamar da fara aikin Hajjinsa a sansanin Alhazai da ke jihar Kano, wanda ya ce zai kuma kammala hajjin nasa a sansanin.

Maniyyacin, Malam Jibrin Abdu, daga karamar hukumar Gezawa ya dauki hankalin mutane bayan da aka hange shi sanye da harami wanda ya nuna fara aikin hajjinsa a sansanin alhazan.

  • Mahara Sun Sace Basarake Da Matar Aure A Kano
  • Hukumar Kashe Gobara A Jihar Kano Ta Ceto Mutum 135 A Watan Yuni

“Ni na fara aikin hajji na tunda akwai dukkan abubuwan da ake bukata a nan, na tabbata zan dawo na kammala aikin, na san yadda ake yi. Wannan ba shi ne zuwana na fari ba, na kuma tabbata ba zai zama na karshe ba,” Inji shi.

Ya kara da cewa, “Na sayar da gonata domin samun zuwa aikin Hajjin, amma wasu shugabannin gangan sun haramta min zuwa hajji,” duk da ya aminta da cewar hakan nufin Allah ne.

Bayan Malam Abdu, ita ma wata mata, Suwaiba Sani, tare da wasu mutane masu yawa, sun yi Allah wadarai tare da dora wannan laifi kan wadanda suka yi sanadin hana su shiga jirgin, wanda cikin fushi suka bayyana cewa ba za su taba yafe wa duk wadanda suke da hannu wajen haramta masu zuwa aikin hajjin ba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rashin ÆŠaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya ÆŠauke Shi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

Wakilin LEADERSHIP Hausa a jihar Kano ya nakalto cewa, a kalla maniyyata 745 ne aka bari a kasa a filin sauka da tashin jiragen sama na Malam Aminu Kano a ranar Alhamis bayan da jirgin karshe ya tashi zuwa kasa mai tsarki da misalin karfe 3:45 na yammacin Alhamis din.

Babban sakataren hukumar Alhazai ta Jihar Kano, Muhammad Abba Danbatta, wanda shi ma bai samu tashi a wannan jirgin ba, tare da sauran daraktoci hukumar, ya alakanta wannan matsala da gazawar hukumar alhazan ta kasa bisa rashin cika alkawarin kamfanin da aka yi alkawarin jigilar alhazan na Azman wanda ya sa har sai da Gwamnatin Saudiyya ta kara tsawaita lokacin daukar alhazan amma duk da hakan sai da aka bar wasu da daman.

Kazalika, LEADERSHIP Hausa ta tabbatar da cewa, bayan jihar Kano din, a jihohin kasar nan da dama an samu matsalar jigilar Alhazai inda wasu maniyyata da dama suka rasa damar zuwa hajjin a bana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Karon Farko, ‘Yan Ta’adda Sun Farmaki Tawagar Buhari

Next Post

Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

Related

Yadda Rashin ÆŠaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya ÆŠauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin ÆŠaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya ÆŠauke Shi

1 week ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

1 month ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

1 month ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri FyaÉ—e A Bauchi

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

3 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in ÆŠansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

4 months ago
Next Post
Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Al'ajabi

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.