• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alakar Sin Da Afirka Na Kara Karko Duk Da Adawar Kasashen Yamma

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Alakar Sin Da Afirka Na Kara Karko Duk Da Adawar Kasashen Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ko da yaushe kasashen yamma na tsarguwa kan sakamakon huldar Sin da Afirka. Masana suna da yakinin cewa, bayan duka mummunan zarge-zarge da hannunka mai sanda da kasashen yamma ke ci gaba da yi kan alakar Sin da Afirka ta hanyar ikirarin cewa, kasar Sin ta dana ma kasashen Afirka “tarkon basussuka”, kasashen yamma sun tsinci kansu a cikin takaici saboda kara ingantuwar alaka tsakanin Sin da Afirka.

Kasancewar ministocin harkokin wajen kasar Sin sun kiyaye al’adar ziyartar Afirka tun daga shekarar 1991, a cikin lokuta masu kyau da ma marasa kyau, na nuni da yadda bangarorin biyu ke mutunta alakar dake tsakaninsu. A tsakiyar shekarar 2023, alal misali, Wang Yi ministan harkokin wajen kasar Sin, wanda kuma mamba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya ziyarci Afirka ta Kudu, Najeriya, Kenya da Habasha kan batutuwa da dama da suka hada da BRICS, da kayayyakin more rayuwa da kuma yafe basussuka. Kuma ministan ya fara ziyarar farko na 2024 a nahiyar daga ranar 13 zuwa 18 ga watan Janairu, inda zai ziyarci kasashen Masar, Tunisia, Togo da Cote d’Ivoire. Daga nan zai zarce zuwa Brazil da Jamaica, kasashe biyu dake da tarihin al’adun Afirka.

  • Ofishin Kula Da Harkokin Taiwan Na Majalisar Gudanarwa Da Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Sun Yi Tsokaci Kan Sakamakon Zabukan Taiwan
  • Yadda Aikin Gine-gine Na Kasar Sin Suka Taimaka Wajen Gudanar Da Gasar Cin Kofin Afirka

Dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka ta kara karfi, yayin da bangarorin biyu ke ci gaba da hadin gwiwa a matakai daban daban, ba wai kawai a fannin tattalin arziki da diflomasiyya ba. A matsayinsu na kasa da nahiya masu tasowa mafi girma, bangarorin biyu suna da kamanceceniya ta fuskar hangen nesa da kalubalen da ya kamata su shawo kansu a bangarori daban-daban, har ma da matakin siyasa.

Domin daidaita hadin gwiwar dake tsakaninsu, bangarorin biyu sun kaddamar da dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka (FOCAC) a shekarar 2000. Dandalin mai wakilai 55 ya kunshi kasar Sin, da kasashen Afirka 53 da ke huldar diflomasiyya da kasar Sin, da kuma Hukumar Tarayyar Afirka. Taron manyan jami’ai karo na 16 na FOCAC da aka gudanar a nan birnin Beijing a watan Oktoban da ya gabata, ya jaddada aniyar bangarorin na samun moriyar juna, da samun ci gaba tare da hadin gwiwar samun nasarori tare. A shekarar 2021, kungiyar ta aiwatar da sama da kashi 70 cikin dari na sakamakon taron kolin FOCAC na Beijing a shekarar 2018.

Dangantakar Sin da Afirka ta kara karfi a lokacin da cutar numfashi ta COVID-19 ta barke. Kasar Sin ta ba da gudummawar kayayyakin jinya da suka hada da kayan aiki, magunguna, ma’aikata da alluran rigakafi na miliyoyin daloli don taimakawa nahiyar ta yaki cutar. Ita ma Afirka ta ba da gudummawa ga yakin da kasar Sin ke yi da cutar ta hanyar ba da goyon baya ta dabi’a da biyayya a farkon annobar. Hakan dai ya faru ne a daidai lokacin da kasashen yamma ke kyamatar kasar Sin tare da neman mayar da kasar Sin saniyar ware. Bayan COVID-19, kasar Sin ta ci gaba da tallafawa tattalin arzikin Afirka ta hanyar inganta harkokin cinikayya da samar da ababen more rayuwa ga nahiyar.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Bisa kididdigar da hukumar kwastam ta kasar Sin ta fitar a watan Agustan shekarar 2023, cinikayya tsakanin Sin da Afirka ya karu da kashi 7.4 cikin dari a duk shekara zuwa kusan dala biliyan 158.36 a rubu’i biyu na farkon shekarar. Kasar Sin ta kasance babbar abokiyar cinikayyar Afirka cikin shekaru goma da suka gabata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar sin da AmurkaAlakar sinbda AfirkaTaiwan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Ƙoli Ta Jingine Hukunci Kan Zaɓen Gwamnan Ribas

Next Post

An Sake Rantsar Da Gwamna Hope Uzodimma A Wa’adi Na Biyu

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

10 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

11 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

12 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

13 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

14 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

16 hours ago
Next Post
Hope uzodimma

An Sake Rantsar Da Gwamna Hope Uzodimma A Wa'adi Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.