ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alkawurana Ga ‘Yan Nijeriya Kan Tsaro, Zaman Kashe Wando Da Tattalin Arziki — Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana irin alkawarukan da zai yi wa ‘yan Nijeriya kan tsaro, zaman kashe wando da kuma bunkasa tattalin arziki, idan har ya zama shugaban Nijeriya a 2023.

Ya ce manufofinsa suna da matukar muhummanci kuma ya ki bayyana ne tun da wuri saboda kar sauran ‘yan takara su yi satan amsa.

ADVERTISEMENT
  • Alhassan Doguwa Ya Musanta Samun Sabani Tsakaninsa Da Ganduje
  • Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben

“Mun jirkinta fito da manufofinmu ne saboda kar sauran ‘yan takara su yi satan amsa. Manufofinmu suna da matukar muhummanci, domin haka ne muke kira ga ‘yan Nijeriya su karanta da kyau tare da yin nazari a kai. Muna bukatar ‘yan Nijeriya su dunga kallon wadannan manufofi a matsayin yarjejeniya tsakanin Kwankwaso/Idahosa da kuma mutane,” in ji shi.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a lokacin da yake bayyana manufofinsa a Abuja ranar Talata da ta gabata, inda ya ce zai fi mayar da hankali ne kan tsaro, ilimi, lafiya, sake fasalin kasa dsa kuma muhalli da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya kara da cewa zai sake maimaita abubuwan da ya yi a Kano wajen kafa kwamiti mai mutum 11 a gunduma da karamar hukuma da kuma matakin tarayya a matsayin hanyan magance rashin tsaro da sauran matsaloli da suka addabi mutane.

Ya kuma ce gwamnatinsa za ta farfado da fasahar zamani wajen ceto Nijeriya, inda ya ce akwai hanyoyin da ake bi wajen tsare kasa daga farmakin cikin gida da na waje.

A cewarsa, zai bai wa hazakun mutane manya-manyan mukamai domin gudanar da aiki yadda ya kamata a kowani bangare.

“A cikin gwamnatinmu, babu wani yaro a Nijeriya da za a hana masa rubuta jarrabawan WAEC, NECO, JAMB da dai sauransu, saboda gwamnati ce za ta biya musu kudin rajista. Wadannan jarrabawa za su kasance kyauta ne, sannan duk wani fom na shiga babban makaranta zai kasance kyauta ne.

“Wadannan hukumomin jarrabawa za su kasance kyauta ne a karkashin gwamnatin Kwankwaso.

“Sakamakon jarrabawa ta JAMB a karkashin gwamnatin Kwankwaso zai kasance na tsawon shekaru hudu kafin wa’adin jarrabawar ya kare,” in ji shi.

Har ila yau, Kwankwaso ya yi alkawarin sake shigar da yara makaranta wadanda aka kora a fadin kasar nan ta hanyar gina ajujuwa 500,000 a dukkan kananan hukumomin Nijeriya guda 774.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
Yadda Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Gudana A Bana

Yadda Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Gudana A Bana

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025
Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

November 15, 2025
Yadda Za Ku Gyara Kanku

Yadda Za Ku Gyara Kanku

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.