• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alkawurana Ga ‘Yan Nijeriya Kan Tsaro, Zaman Kashe Wando Da Tattalin Arziki — Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Alkawurana Ga ‘Yan Nijeriya Kan Tsaro, Zaman Kashe Wando Da Tattalin Arziki — Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana irin alkawarukan da zai yi wa ‘yan Nijeriya kan tsaro, zaman kashe wando da kuma bunkasa tattalin arziki, idan har ya zama shugaban Nijeriya a 2023.

Ya ce manufofinsa suna da matukar muhummanci kuma ya ki bayyana ne tun da wuri saboda kar sauran ‘yan takara su yi satan amsa.

  • Alhassan Doguwa Ya Musanta Samun Sabani Tsakaninsa Da Ganduje
  • Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben

“Mun jirkinta fito da manufofinmu ne saboda kar sauran ‘yan takara su yi satan amsa. Manufofinmu suna da matukar muhummanci, domin haka ne muke kira ga ‘yan Nijeriya su karanta da kyau tare da yin nazari a kai. Muna bukatar ‘yan Nijeriya su dunga kallon wadannan manufofi a matsayin yarjejeniya tsakanin Kwankwaso/Idahosa da kuma mutane,” in ji shi.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a lokacin da yake bayyana manufofinsa a Abuja ranar Talata da ta gabata, inda ya ce zai fi mayar da hankali ne kan tsaro, ilimi, lafiya, sake fasalin kasa dsa kuma muhalli da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya kara da cewa zai sake maimaita abubuwan da ya yi a Kano wajen kafa kwamiti mai mutum 11 a gunduma da karamar hukuma da kuma matakin tarayya a matsayin hanyan magance rashin tsaro da sauran matsaloli da suka addabi mutane.

Ya kuma ce gwamnatinsa za ta farfado da fasahar zamani wajen ceto Nijeriya, inda ya ce akwai hanyoyin da ake bi wajen tsare kasa daga farmakin cikin gida da na waje.

A cewarsa, zai bai wa hazakun mutane manya-manyan mukamai domin gudanar da aiki yadda ya kamata a kowani bangare.

“A cikin gwamnatinmu, babu wani yaro a Nijeriya da za a hana masa rubuta jarrabawan WAEC, NECO, JAMB da dai sauransu, saboda gwamnati ce za ta biya musu kudin rajista. Wadannan jarrabawa za su kasance kyauta ne, sannan duk wani fom na shiga babban makaranta zai kasance kyauta ne.

“Wadannan hukumomin jarrabawa za su kasance kyauta ne a karkashin gwamnatin Kwankwaso.

“Sakamakon jarrabawa ta JAMB a karkashin gwamnatin Kwankwaso zai kasance na tsawon shekaru hudu kafin wa’adin jarrabawar ya kare,” in ji shi.

Har ila yau, Kwankwaso ya yi alkawarin sake shigar da yara makaranta wadanda aka kora a fadin kasar nan ta hanyar gina ajujuwa 500,000 a dukkan kananan hukumomin Nijeriya guda 774.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023AlkawuraKwankwasotakaraZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsegunta Barazanar Tsaro Daga Ofishin Jakadancin Amurka: Wa Abin Zai Amfanar?

Next Post

Yadda Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Gudana A Bana

Related

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

5 minutes ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

4 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

7 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

15 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

21 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

24 hours ago
Next Post
Yadda Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Gudana A Bana

Yadda Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Gudana A Bana

LABARAI MASU NASABA

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.