ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben

by Sadiq
4 years ago
PDP

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna, ta soke zaben fidda gwanin da jam’iyyar PDP ta gudanar a mazabar Kaduna ta tsakiya sakamakon wasu kurakurai. 

Kotun ta umarci jam’iyyar PDP da ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani na dan takarar Sanata na jam’iyyar a cikin kwanaki 14.

  • An Mayar Da Tubabbun Mayakan Boko Haram 3,500 Unguwanninsu A Jihar Borno
  • Rashin Tsaro: Buhari Ya Kalubalanci ‘Yansanda A Kan Matsalar Tsaro 

Mai shari’a Muhammed Garba Umar na babbar kotun tarayya da ke Kaduna, wanda ya yanke hukunci a ranar Laraba a kan shari’ar ya ce “Duk korafe-korafen da mai shigar da karar ya yi na da yawa, haka ma hukuncin da INEC ta yanke na gudanar da sabon zaben fidda gwani da ba a yi ba daga baya, kamar yadda sakamakon ya gudana, ikirarin da wanda ake tuhuma ya yi watsi da shi.”

ADVERTISEMENT

Mai shigar da karar, Usman Ibrahim, ta bakin lauyansa, Samuel Atung, (SAN), ya garzaya kotu yana kalubalantar fitowar Lawal Adamu a kan rashin kuri’ar da aka kada masa, inda ya roki kotun da ta rushe wannan zaben tare da bai wa duk wani mai bukata dama daidai gwargwado don gwada farin jininsa.

Atung ya bayar da hujjar cewa wanda yake karewa yana da faifan bidiyo da bayanan da suka nuna cewa wakilai sun kada kuri’a wadanda sakamakon shari’ar da ya yi nuni da su shi ne rushe sakamakon zaben fidda gwanin da kuma soke sakamakon zaben, inda ya kara da cewa majalisar zartaswar jam’iyyar PDP ta kasa ta nemi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Hukumar INEC ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani kawai don wanda ya karewa ya tattaro mabiyansa zuwa wurin da aka yi zaben a banza.

Lauyan Usman Ibrahim, Samuel Atung, (SAN) da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan yanke hukuncin, ya tabbatar da cewa kotun ta zartar da hukunci ne bayan nazari da ta yi.

Atung ya ce, “Bayan da jam’iyyar PDP ta Kaduna ta tsakiya ta zabi dan takararta a zaben 2023, abokin takararmu ya rubuta koke ga kwamitin daukaka kara na jam’iyyar yana kalubalantar sakamakon zaben.

“Muna da hujjojin bidiyo kan hakan kuma kwamitin ya yi la’akari da rokon da muka gabatar kuma ya mika shawararsa ga kwamitin zaben wanda a cikin hikimarsa ya yi kira da a sake zaben fidda gwanin.

“Jam’iyyar PDP ta rubuta wa INEC wasika, ta sanar da ‘yansandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da sauran masu ruwa da tsaki game da matakin da ta dauka na sake gudanar da zaben fidda gwanin na shiyyar Sanata Kaduna ta tsakiya, wanda abin farin ciki ne.

“Abin takaici a ranar da aka saka, abokin aikinmu, bayan ya tattaro magoya bayansa zuwa wurin da za a sake zaben fidda gwanin, sai aka ce ba za a ci gaba da gudanar da zaben ba saboda yadda mahukuntan suka ba da umarni.

“Mun zo kotu ne muna neman adalci a wannan takin kuma alkali ya yanke hukuncin cewa jam’iyyar ta bi matakin da kwamitin kasa ya dauka sannan ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwanin nan da makonni biyu.”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.