ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alkawurana Ga ‘Yan Nijeriya Kan Tsaro, Zaman Kashe Wando Da Tattalin Arziki — Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana irin alkawarukan da zai yi wa ‘yan Nijeriya kan tsaro, zaman kashe wando da kuma bunkasa tattalin arziki, idan har ya zama shugaban Nijeriya a 2023.

Ya ce manufofinsa suna da matukar muhummanci kuma ya ki bayyana ne tun da wuri saboda kar sauran ‘yan takara su yi satan amsa.

ADVERTISEMENT
  • Alhassan Doguwa Ya Musanta Samun Sabani Tsakaninsa Da Ganduje
  • Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben

“Mun jirkinta fito da manufofinmu ne saboda kar sauran ‘yan takara su yi satan amsa. Manufofinmu suna da matukar muhummanci, domin haka ne muke kira ga ‘yan Nijeriya su karanta da kyau tare da yin nazari a kai. Muna bukatar ‘yan Nijeriya su dunga kallon wadannan manufofi a matsayin yarjejeniya tsakanin Kwankwaso/Idahosa da kuma mutane,” in ji shi.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a lokacin da yake bayyana manufofinsa a Abuja ranar Talata da ta gabata, inda ya ce zai fi mayar da hankali ne kan tsaro, ilimi, lafiya, sake fasalin kasa dsa kuma muhalli da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya kara da cewa zai sake maimaita abubuwan da ya yi a Kano wajen kafa kwamiti mai mutum 11 a gunduma da karamar hukuma da kuma matakin tarayya a matsayin hanyan magance rashin tsaro da sauran matsaloli da suka addabi mutane.

Ya kuma ce gwamnatinsa za ta farfado da fasahar zamani wajen ceto Nijeriya, inda ya ce akwai hanyoyin da ake bi wajen tsare kasa daga farmakin cikin gida da na waje.

A cewarsa, zai bai wa hazakun mutane manya-manyan mukamai domin gudanar da aiki yadda ya kamata a kowani bangare.

“A cikin gwamnatinmu, babu wani yaro a Nijeriya da za a hana masa rubuta jarrabawan WAEC, NECO, JAMB da dai sauransu, saboda gwamnati ce za ta biya musu kudin rajista. Wadannan jarrabawa za su kasance kyauta ne, sannan duk wani fom na shiga babban makaranta zai kasance kyauta ne.

“Wadannan hukumomin jarrabawa za su kasance kyauta ne a karkashin gwamnatin Kwankwaso.

“Sakamakon jarrabawa ta JAMB a karkashin gwamnatin Kwankwaso zai kasance na tsawon shekaru hudu kafin wa’adin jarrabawar ya kare,” in ji shi.

Har ila yau, Kwankwaso ya yi alkawarin sake shigar da yara makaranta wadanda aka kora a fadin kasar nan ta hanyar gina ajujuwa 500,000 a dukkan kananan hukumomin Nijeriya guda 774.

Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Yadda Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Gudana A Bana

Yadda Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Gudana A Bana

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.