• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alkawurana Ga ‘Yan Nijeriya Kan Tsaro, Zaman Kashe Wando Da Tattalin Arziki — Kwankwaso

byYusuf Shuaibu
3 years ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana irin alkawarukan da zai yi wa ‘yan Nijeriya kan tsaro, zaman kashe wando da kuma bunkasa tattalin arziki, idan har ya zama shugaban Nijeriya a 2023.

Ya ce manufofinsa suna da matukar muhummanci kuma ya ki bayyana ne tun da wuri saboda kar sauran ‘yan takara su yi satan amsa.

  • Alhassan Doguwa Ya Musanta Samun Sabani Tsakaninsa Da Ganduje
  • Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben

“Mun jirkinta fito da manufofinmu ne saboda kar sauran ‘yan takara su yi satan amsa. Manufofinmu suna da matukar muhummanci, domin haka ne muke kira ga ‘yan Nijeriya su karanta da kyau tare da yin nazari a kai. Muna bukatar ‘yan Nijeriya su dunga kallon wadannan manufofi a matsayin yarjejeniya tsakanin Kwankwaso/Idahosa da kuma mutane,” in ji shi.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a lokacin da yake bayyana manufofinsa a Abuja ranar Talata da ta gabata, inda ya ce zai fi mayar da hankali ne kan tsaro, ilimi, lafiya, sake fasalin kasa dsa kuma muhalli da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya kara da cewa zai sake maimaita abubuwan da ya yi a Kano wajen kafa kwamiti mai mutum 11 a gunduma da karamar hukuma da kuma matakin tarayya a matsayin hanyan magance rashin tsaro da sauran matsaloli da suka addabi mutane.

Ya kuma ce gwamnatinsa za ta farfado da fasahar zamani wajen ceto Nijeriya, inda ya ce akwai hanyoyin da ake bi wajen tsare kasa daga farmakin cikin gida da na waje.

A cewarsa, zai bai wa hazakun mutane manya-manyan mukamai domin gudanar da aiki yadda ya kamata a kowani bangare.

“A cikin gwamnatinmu, babu wani yaro a Nijeriya da za a hana masa rubuta jarrabawan WAEC, NECO, JAMB da dai sauransu, saboda gwamnati ce za ta biya musu kudin rajista. Wadannan jarrabawa za su kasance kyauta ne, sannan duk wani fom na shiga babban makaranta zai kasance kyauta ne.

“Wadannan hukumomin jarrabawa za su kasance kyauta ne a karkashin gwamnatin Kwankwaso.

“Sakamakon jarrabawa ta JAMB a karkashin gwamnatin Kwankwaso zai kasance na tsawon shekaru hudu kafin wa’adin jarrabawar ya kare,” in ji shi.

Har ila yau, Kwankwaso ya yi alkawarin sake shigar da yara makaranta wadanda aka kora a fadin kasar nan ta hanyar gina ajujuwa 500,000 a dukkan kananan hukumomin Nijeriya guda 774.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Yadda Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Gudana A Bana

Yadda Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Gudana A Bana

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version