• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Allah Ya Yi Wa Aminu Dantata Arzikin Da Al’umma Suka Amfana Da Shi – Abubakar

by Ibrahim Muhammad
4 months ago
Dantata

Tsohon dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Birnin Kano, Hon. Abubakar Nuhu Danfulan Danburan ya bayyana cewa Allah ya yi wa Alhaji Aminu Dantata arzikin da al’umma suka amfana da shi.

Ya ce, “Wannan rashi da aka yi na Alhaji Aminu Dantata, rashi ne babba na Uba, shugaba, abin alfahari gare mu, ba rashi ba ne ga Jihar Kano ita kadai ba har da kasa baki daya da al’ummar musulman duniya wannan rashi ya shafesu gaba daya, Allah ya gafarta masa ya ba shi aljanna”

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda

Hon Abubakar ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida.

Ya ce shi ne irin mutumin da ake cewa Allah ya yi masa arziki wanda kowa zai yi fata ya yi koyi da irin abubuwan da ya yi na rayuwa a duniya da arzikinsa da wadatarsa sun amfani ba wai kawai ga iyalansa, jikokinsa ko surukansa ba har al’umma da ‘yan’uwa da abokan arziki da kuma al’ummar musulman na duniya.

Ya kara da cewa domin ya amfanar da abubuwa da yawa na taimakon da ya yi, wanda sai yanzu ne wasu suke ta fitowa, ya yi wasu abubuwa tsakaninsa da Allah, daya daga cikin sakamako da wannan abubuwa suka haifar masa shi ne, na yadda aka yi jana’izarsa a Madina kusa da Annabi, wannan ba karamar daraja ba ce Allah ya nuna masa tun daga duniya.

LABARAI MASU NASABA

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Hon Abubakar ya ce ba zai taba mantawa ba haduwarsu da Alhaji Aminu Dantata na karshe ita ce ranar karamar Sallah, ya je wajensa a Makka bayan an kammala Azumi, a nan ya yi idi, shi kuma Allah ya kai shi Makka a wannan lokaci da ma duk shekara yakan kai masa ziyara ya gaishe shi, wani abin ban sha’awa a rayuwarsa duk da yawan shekarunsa, Allah bai sa baya gane jama’a ba, yana da lafiyar yin magana ga mutane har ya janyo barkwanci.

Ya ce baiwar da Allah ya yi wa Aminu Dantata na gane jama’a a tsawo shekaru sama da 90, ba karamar baiwa ba ce, sai dai kullum abin da yake fada mana shi ne, “ku saka hakuri a rayuwa ku, ku zama mutane masu rike amana da gaskiya duk abin da za mu yi, mu yi don Allah, mu tsaya mu taimaka addininmu”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Labarai

Hukumar NASENI

October 25, 2025
Next Post
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

LABARAI MASU NASABA

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025

Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.