ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Allah Ya Yi Wa Aminu Dantata Arzikin Da Al’umma Suka Amfana Da Shi – Abubakar

by Ibrahim Muhammad
11 months ago
Dantata

Tsohon dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Birnin Kano, Hon. Abubakar Nuhu Danfulan Danburan ya bayyana cewa Allah ya yi wa Alhaji Aminu Dantata arzikin da al’umma suka amfana da shi.

Ya ce, “Wannan rashi da aka yi na Alhaji Aminu Dantata, rashi ne babba na Uba, shugaba, abin alfahari gare mu, ba rashi ba ne ga Jihar Kano ita kadai ba har da kasa baki daya da al’ummar musulman duniya wannan rashi ya shafesu gaba daya, Allah ya gafarta masa ya ba shi aljanna”

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda

Hon Abubakar ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida.

ADVERTISEMENT

Ya ce shi ne irin mutumin da ake cewa Allah ya yi masa arziki wanda kowa zai yi fata ya yi koyi da irin abubuwan da ya yi na rayuwa a duniya da arzikinsa da wadatarsa sun amfani ba wai kawai ga iyalansa, jikokinsa ko surukansa ba har al’umma da ‘yan’uwa da abokan arziki da kuma al’ummar musulman na duniya.

Ya kara da cewa domin ya amfanar da abubuwa da yawa na taimakon da ya yi, wanda sai yanzu ne wasu suke ta fitowa, ya yi wasu abubuwa tsakaninsa da Allah, daya daga cikin sakamako da wannan abubuwa suka haifar masa shi ne, na yadda aka yi jana’izarsa a Madina kusa da Annabi, wannan ba karamar daraja ba ce Allah ya nuna masa tun daga duniya.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Hon Abubakar ya ce ba zai taba mantawa ba haduwarsu da Alhaji Aminu Dantata na karshe ita ce ranar karamar Sallah, ya je wajensa a Makka bayan an kammala Azumi, a nan ya yi idi, shi kuma Allah ya kai shi Makka a wannan lokaci da ma duk shekara yakan kai masa ziyara ya gaishe shi, wani abin ban sha’awa a rayuwarsa duk da yawan shekarunsa, Allah bai sa baya gane jama’a ba, yana da lafiyar yin magana ga mutane har ya janyo barkwanci.

Ya ce baiwar da Allah ya yi wa Aminu Dantata na gane jama’a a tsawo shekaru sama da 90, ba karamar baiwa ba ce, sai dai kullum abin da yake fada mana shi ne, “ku saka hakuri a rayuwa ku, ku zama mutane masu rike amana da gaskiya duk abin da za mu yi, mu yi don Allah, mu tsaya mu taimaka addininmu”.

Dantata
Ibrahim Muhammad
+ postsBio
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Muna Farin Ciki Da Karramawar Da Gwamna Abba Ke Samu Saboda Aiki Tukuru – Hon. Ibrahim
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.