• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Ministar Jinkai Ta Kaddamar Da Rabon Tallafi Ga Mutum 5,428 A Neja

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Ambaliyar Ruwa: Ministar Jinkai Ta Kaddamar Da Rabon Tallafi Ga Mutum 5,428 A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta ƙaddamar da shirin nan na Gwamnatin Tarayya na raba kuɗin tallafi ga mabuƙata mutum 5,428 a Jihar Neja.

 

Ministar ta ƙaddamar da shirin ne a Gidan Gwamnatin jihar da ke Minna a ranar Talata.

  • Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

A taron ƙaddamarwar, ta yi amfani da wannan damar ta jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar ta Neja kan ibtila’in ambaliyar ruwa da ya same su a kwanan baya.

 

Labarai Masu Nasaba

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

Daga nan ta ba da shawara ga waɗanda za su ci moriyar shirin da su yi amfani da kuɗin tallafin ta hanyar da ta dace domin su inganta rayuwar su ta yau da kullum, sa’annan ta ce kuɗin za su taimaka wa waɗanda bala’in ambaliyar ruwan ya shafa wajen samun sauƙi.

Ministar Jinƙai
Minista Sadiya Umar Farouq tare da Sakataren Gwamnatin Jiha, Alhaji Ahmed Matane, da wasu masu cin moriyar shirin

Hajiya Sadiya ta ce: “Burin mu a Jihar Neja shi ne mu raba tallafin tsabar kuɗin ga gungu-gungun mabuƙata mutum 5,428 da aka samo daga yankunan ƙananan hukumomi 25 da ke faɗin jihar.

 

Ta bayyana cewa: “Shugaba Muhammadu Buhari, ta hanyar tsarin da ya fito da shi na taimaka wa kowa da kowa a al’umma, ya ba da umarnin cewa a tabbatar kashi 70 cikin ɗari na masu cin moriyar wannan shirin su kasance mata ne, sannan sauran kashi 30 cikin ɗari kuma su kasance matasa ne.

 

“Haka kuma ya ba da umarnin cewa a ware aƙalla kashi 15 cikin ɗari na jimillar masu cin moriyar shirin su kasance ‘yan ƙasar nan ne masu buƙatu na musamman, wato irin su naƙasassu da kuma tsofaffi tukuf a jihar.

 

“Ana matuƙar fatar cewa waɗanda za su fara cin moriyar shirin za su yi amfani da wannan tallafi wajen inganta rayuwar su, su nemi arziki, su samar da guraben aikin yi, su ɗaga matsayin rayuwar su.”

 

Ministar ta kuma miƙa kayan abinci da waɗanda ba na abinci ba ga waɗanda ambaliyar ruwan nan ta shafa, sannan ta ba da tabbacin cewa gwamnati za ta ci gaba da agaza wa mabuƙata kamar yadda Shugaba Muhammadu Buhari ya umarta.

 

A taron, har ila yau, ministar ta ƙaddamar da shirin nan na tallafi na Gwamnatin Tarayya mai taken ‘Government Enterprise Empowerment Programme’ (GEEP) inda aka samu mutum 3,166 da za a ba bashi mara ruwa da ya kama tsakanin N50,000 zuwa N300,000 kowane mutum ɗaya.

 

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Neja, Alhaji Abubakar Sani-Bello, ya gode wa Gwamnatin Tarayya da ita kan ta ministar saboda waɗannan shirye-shirye na haɓaka tattalin arzikin ƙasa. A cewar sa, sama da mutum miliyan ɗaya ne aka tsamo daga ƙangin fatara a ƙasar nan ta hanyar su.

 

Sani-Bello, wanda ya samu wakilci daga Sakataren Gwamnatin Jihar Neja, Alhaji Ahmed Matane, ya yi kira ga ma’aikatar Harkokin Jinƙai, da ta Harkokin Mata da ta Aikin Gona da kuma ta Matasa da Wasanni da su riƙa bin diddigin waɗanda su ka ci moriyar shirye-shiryen haɓaka rayuwa da ke ƙarƙashin su domin su tabbatar da cigaba da kuma nasarorin da ake samu daga wannan lokaci zuwa wannan lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya Na Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Sabbin Takardun Kudin Da Aka Kaddamar

Next Post

Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Zai Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Ranar Litinin Mai Zuwa

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

6 minutes ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

59 minutes ago
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

2 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

4 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

15 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

17 hours ago
Next Post
Sati 3 Masu Zuwa Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Zai Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa

Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Zai Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Ranar Litinin Mai Zuwa

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.