ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Ministar Jinkai Ta Kaddamar Da Rabon Tallafi Ga Mutum 5,428 A Neja

by Sulaiman
4 years ago
Ministar Jinƙai

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta ƙaddamar da shirin nan na Gwamnatin Tarayya na raba kuɗin tallafi ga mabuƙata mutum 5,428 a Jihar Neja.

 

Ministar ta ƙaddamar da shirin ne a Gidan Gwamnatin jihar da ke Minna a ranar Talata.

ADVERTISEMENT
  • Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

A taron ƙaddamarwar, ta yi amfani da wannan damar ta jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar ta Neja kan ibtila’in ambaliyar ruwa da ya same su a kwanan baya.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Daga nan ta ba da shawara ga waɗanda za su ci moriyar shirin da su yi amfani da kuɗin tallafin ta hanyar da ta dace domin su inganta rayuwar su ta yau da kullum, sa’annan ta ce kuɗin za su taimaka wa waɗanda bala’in ambaliyar ruwan ya shafa wajen samun sauƙi.

Ministar Jinƙai
Minista Sadiya Umar Farouq tare da Sakataren Gwamnatin Jiha, Alhaji Ahmed Matane, da wasu masu cin moriyar shirin

Hajiya Sadiya ta ce: “Burin mu a Jihar Neja shi ne mu raba tallafin tsabar kuɗin ga gungu-gungun mabuƙata mutum 5,428 da aka samo daga yankunan ƙananan hukumomi 25 da ke faɗin jihar.

 

Ta bayyana cewa: “Shugaba Muhammadu Buhari, ta hanyar tsarin da ya fito da shi na taimaka wa kowa da kowa a al’umma, ya ba da umarnin cewa a tabbatar kashi 70 cikin ɗari na masu cin moriyar wannan shirin su kasance mata ne, sannan sauran kashi 30 cikin ɗari kuma su kasance matasa ne.

 

“Haka kuma ya ba da umarnin cewa a ware aƙalla kashi 15 cikin ɗari na jimillar masu cin moriyar shirin su kasance ‘yan ƙasar nan ne masu buƙatu na musamman, wato irin su naƙasassu da kuma tsofaffi tukuf a jihar.

 

“Ana matuƙar fatar cewa waɗanda za su fara cin moriyar shirin za su yi amfani da wannan tallafi wajen inganta rayuwar su, su nemi arziki, su samar da guraben aikin yi, su ɗaga matsayin rayuwar su.”

 

Ministar ta kuma miƙa kayan abinci da waɗanda ba na abinci ba ga waɗanda ambaliyar ruwan nan ta shafa, sannan ta ba da tabbacin cewa gwamnati za ta ci gaba da agaza wa mabuƙata kamar yadda Shugaba Muhammadu Buhari ya umarta.

 

A taron, har ila yau, ministar ta ƙaddamar da shirin nan na tallafi na Gwamnatin Tarayya mai taken ‘Government Enterprise Empowerment Programme’ (GEEP) inda aka samu mutum 3,166 da za a ba bashi mara ruwa da ya kama tsakanin N50,000 zuwa N300,000 kowane mutum ɗaya.

 

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Neja, Alhaji Abubakar Sani-Bello, ya gode wa Gwamnatin Tarayya da ita kan ta ministar saboda waɗannan shirye-shirye na haɓaka tattalin arzikin ƙasa. A cewar sa, sama da mutum miliyan ɗaya ne aka tsamo daga ƙangin fatara a ƙasar nan ta hanyar su.

 

Sani-Bello, wanda ya samu wakilci daga Sakataren Gwamnatin Jihar Neja, Alhaji Ahmed Matane, ya yi kira ga ma’aikatar Harkokin Jinƙai, da ta Harkokin Mata da ta Aikin Gona da kuma ta Matasa da Wasanni da su riƙa bin diddigin waɗanda su ka ci moriyar shirye-shiryen haɓaka rayuwa da ke ƙarƙashin su domin su tabbatar da cigaba da kuma nasarorin da ake samu daga wannan lokaci zuwa wannan lokaci.

Ministar Jinƙai
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
Sati 3 Masu Zuwa Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Zai Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa

Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Zai Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Ranar Litinin Mai Zuwa

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.