• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Ambaliya

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da cewa ambaliyar ruwa ta mamaye a ƙalla unguwanni tara a ƙananan hukumomin Ibaji da Kogi, inda ta lalata gonaki da gidaje tare da raba dubban jama’a da muhallansu. Sakataren hukumar agajin gaggawa ta jihar (SEMA), Mukhtar Atima, ya bayyana hakan a Lokoja, inda ya ce an buɗe sansanonin rikon ƙwarya 42 domin sauƙaƙa wa waɗanda abin ya shafa.

Rahotanni sun nuna cewa a shekarar 2024, ambaliya ta tilasta wa mutane sama da miliyan biyu barin gidajensu a ƙananan hukumomi tara na jihar. Wannan ya jawo lalacewar makarantu, da asibitoci, da hanyoyi, da gadoji, da kuma lalata gonaki, inda manoma musamman masu noman doya suka fi fuskantar asara mai girma. Wasu daga cikinsu sun yi gaggawar girbi kafin lokacin da ya dace don guje wa asarar jarinsu, musamman waɗanda suka karɓi bashi daga bankuna.

  • Jihar Kogi Na Cikin Fargaba Yayin Da Kogin Neja Da Benuwe Suka Tumfatsa
  • Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

A wasu sassan jihar, ambaliya ta katse manyan hanyoyin shiga da fita, lamarin da ya ƙara tsananta wahalar kai ɗauki. Shugaban ƙungiyar ci gaban Kupa (KUDA), Sa’idu Bn Malik, ya ce ambaliyar ta durƙusar da tattalin arziƙin yankin, ta lalata hanyoyin mota, kuma ta ƙara jefa al’umma cikin barazanar kamuwa da rashin lafiya da jawo rashin tsaro.

A jihar Legas kuwa, ruwan sama mai yawa ya rufe muhimman unguwanni ciki har da Lekki, da Mile 2, da 3rd Mainland Bridge, da Ago Palace. Jama’a sun koka da toshewar magudanan ruwa da kuma rashin gaggawar gwamnatin jihar wajen bada agaji.

Daily Trust ta rawaito cewa, Mazauna yankunan sun ce harkokin sufuri sun tsaya cak, gidaje da kadarori sun lalace, yayin da aka tilasta wa wasu barin motoci su yi tafiya a ƙafa. Wasu kuma sun bayyana yadda aikin gina hanya a Lekki ya kara tsananta cunkoso da halin da ake ciki.

LABARAI MASU NASABA

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 
Labarai

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano
Labarai

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar
Labarai

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.