• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

by Sani Anwar
1 year ago
in Kiwon Lafiya
0
Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka sani ne, Mangwaro na dauke da sinadarin ‘bitamin da minerals’ masu yawan gaske, wadanda mace mai juna biyu ke bukata a lokacin da take dauke da ciki, domin karfafa jikinta da kuma kula da lafiyar abin da ke cikinta.

Sai dai, ana shawarartar mai juna biyun da kada ta sha wannan mangwaro fiye da guda daya a kowace rana. Sannan, amfanin nasa ga masu juna biyun sun hada da:

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • Rikicin Sarautar Kano: Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnatin Tarayya, APC Ta Mayar Da Martani

– Mangoro na bai wa mata masu dauke da juna biyu kariya daga karancin jini, sakamakon wadataccen sinadarin ‘iron’ da yake da shi, sannan kuma yana kara yawan samar da jinin cikin bargo.

– Haka nan, yana taimaka wa jaririn da ke cikin ciki; ya yi girma cikin koshin lafiya, saboda yana dauke da wadataccen sinadarin ‘folic acid’, wanda ke taimakawa wajen ci gaban girman jaririn da yake cikin cikin uwa.

– Shan mangwaro a cikin watan farkon daukar ciki, abu ne mai matukar muhimmanci da yake taimakawa wajen saurin girman jijiyoyin sadarwa (nerbes).

Labarai Masu Nasaba

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

– Kazalika, yana taimaka wa mata masu ciki; don kawar da matsalolin cushewar ciki, wadanda mata masu juna biyu ke fama da shi sosai, domin kuwa yana dauke da ‘dietary fiber’; wanda ke taimakawa wajen inganta aikin tsarin narkewar abinci.

Tunatarwa:

– Ya kamata mata masu juna biyu su kula, sannan kuma su sani cewa akwai mangwaron da ba na asali ba, ‘yan dabaru aka yi masa don sayar a samu kudi.

– Saboda haka, wajibi ne masu juna biyu su guji amfani da mangwaron da ba na asali ba, ma’ana irin wanda ake sa wa wani sinadari ya yi saurin nuna, domin kuwa ko shakka babu wannan na iya haifar da illa ga lafiyarsu da kuma abin da ke cikin cikinsu.

– Har ila yau, mangwaron yana dauke da wani sinadari mai suna ‘calcium carbide’, wato wani sinadari ne da ake amfani da shi wajen samar da dan itaciya ta hanyar da ba ta dabi’a ba (artificially), wanda hakan na iya karawa mai juna biyu da abin da yake cikin cikinta damar cudanya da sinadarin ‘arsenic da phosphorus’ masu cutarwa.

Haka zalika, akwai illoli masu dimbin yawa da mata masu juna biyu ke fuskanta yayin da suka sha mangwaron da ba na dabi’a bad a suka hada da kamar haka:

– Gudawa

– Chanzawar yanayi

– Ciwon kai

– Jiri ko juwa

– Ciwon ciki

Har wa yau, daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen guje wa amfani da mangwaron da ba na dabi’a ba shi ne, ta hanyar amfani da mangwaron a lokacin kakarsa, ma’ana lokacin da muka sani na asali; wanda a ciki ake girbin mangwaron, sannan kuma mu kauracewa amfani da mangwaron da ake samar da shi bayan kakarsa ta wuce.

Ya Allah ka sauki duk wata mace mai juna biyu lafiya cikin aminci.

Daga kundin Bashir Suraj Adam


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LafiyaMai Juna BiyuMangwaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Najeriya Sun Gana A Beijing

Next Post

Atiku Ya Ziyarci Buhari Da Sarkin Daura Da Kuma Sarkin Katsina

Related

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
Kiwon Lafiya

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

4 days ago
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
Kiwon Lafiya

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

2 weeks ago
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa
Kiwon Lafiya

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

2 weeks ago
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani
Kiwon Lafiya

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

4 weeks ago
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
Kiwon Lafiya

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

4 weeks ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

1 month ago
Next Post
Atiku Ya Ziyarci Buhari Da Sarkin Daura Da Kuma Sarkin Katsina

Atiku Ya Ziyarci Buhari Da Sarkin Daura Da Kuma Sarkin Katsina

LABARAI MASU NASABA

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.