ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

by Sani Anwar
1 year ago
Mangwaro

Kamar yadda aka sani ne, Mangwaro na dauke da sinadarin ‘bitamin da minerals’ masu yawan gaske, wadanda mace mai juna biyu ke bukata a lokacin da take dauke da ciki, domin karfafa jikinta da kuma kula da lafiyar abin da ke cikinta.

Sai dai, ana shawarartar mai juna biyun da kada ta sha wannan mangwaro fiye da guda daya a kowace rana. Sannan, amfanin nasa ga masu juna biyun sun hada da:

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • Rikicin Sarautar Kano: Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnatin Tarayya, APC Ta Mayar Da Martani

– Mangoro na bai wa mata masu dauke da juna biyu kariya daga karancin jini, sakamakon wadataccen sinadarin ‘iron’ da yake da shi, sannan kuma yana kara yawan samar da jinin cikin bargo.

ADVERTISEMENT

– Haka nan, yana taimaka wa jaririn da ke cikin ciki; ya yi girma cikin koshin lafiya, saboda yana dauke da wadataccen sinadarin ‘folic acid’, wanda ke taimakawa wajen ci gaban girman jaririn da yake cikin cikin uwa.

– Shan mangwaro a cikin watan farkon daukar ciki, abu ne mai matukar muhimmanci da yake taimakawa wajen saurin girman jijiyoyin sadarwa (nerbes).

LABARAI MASU NASABA

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

– Kazalika, yana taimaka wa mata masu ciki; don kawar da matsalolin cushewar ciki, wadanda mata masu juna biyu ke fama da shi sosai, domin kuwa yana dauke da ‘dietary fiber’; wanda ke taimakawa wajen inganta aikin tsarin narkewar abinci.

Tunatarwa:

– Ya kamata mata masu juna biyu su kula, sannan kuma su sani cewa akwai mangwaron da ba na asali ba, ‘yan dabaru aka yi masa don sayar a samu kudi.

– Saboda haka, wajibi ne masu juna biyu su guji amfani da mangwaron da ba na asali ba, ma’ana irin wanda ake sa wa wani sinadari ya yi saurin nuna, domin kuwa ko shakka babu wannan na iya haifar da illa ga lafiyarsu da kuma abin da ke cikin cikinsu.

– Har ila yau, mangwaron yana dauke da wani sinadari mai suna ‘calcium carbide’, wato wani sinadari ne da ake amfani da shi wajen samar da dan itaciya ta hanyar da ba ta dabi’a ba (artificially), wanda hakan na iya karawa mai juna biyu da abin da yake cikin cikinta damar cudanya da sinadarin ‘arsenic da phosphorus’ masu cutarwa.

Haka zalika, akwai illoli masu dimbin yawa da mata masu juna biyu ke fuskanta yayin da suka sha mangwaron da ba na dabi’a bad a suka hada da kamar haka:

– Gudawa

– Chanzawar yanayi

– Ciwon kai

– Jiri ko juwa

– Ciwon ciki

Har wa yau, daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen guje wa amfani da mangwaron da ba na dabi’a ba shi ne, ta hanyar amfani da mangwaron a lokacin kakarsa, ma’ana lokacin da muka sani na asali; wanda a ciki ake girbin mangwaron, sannan kuma mu kauracewa amfani da mangwaron da ake samar da shi bayan kakarsa ta wuce.

Ya Allah ka sauki duk wata mace mai juna biyu lafiya cikin aminci.

Daga kundin Bashir Suraj Adam

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha
Kiwon Lafiya

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
Kiwon Lafiya

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

October 11, 2025
Next Post
Atiku Ya Ziyarci Buhari Da Sarkin Daura Da Kuma Sarkin Katsina

Atiku Ya Ziyarci Buhari Da Sarkin Daura Da Kuma Sarkin Katsina

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.