ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sarautar Kano: Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnatin Tarayya, APC Ta Mayar Da Martani

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kano

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya zargi gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC kan amsar munanan shawarwari daga makiyan Jihar Kano.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a yayin bikin kaddamar da aikin gina titunan mai tsawon kilomita 82 a mahaifarsa ta Madobi da gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin

Zargin ya biyo bayan rikicin masarautar Kano, inda rahotanni suna nuna cewa hukumomin tsaro na tarayya na goyon bayan hambararren Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero.

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan Jihar Kano, ya jaddada cewa al’ummar Jihar Kano ba za su lamunci duk wani yunkurin yin katsalandan a cikin harkokin da suka jibanci jihar.

“Muna da yawan mabiya domin mutane sun yarda da mu. Sannan kuma mu masu goyon bayan jama’a ne, kuma gwamnatin NNPP ta kudiri aniyar yi musu hidima tun da suka zabe ta,” in ji Kwankwaso.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ya kuma jaddada kudirin ‘yan Jihar Kano na mara wa gwamnan jihar baya domin cimma burin da ta sa a gaba duk da cewa ana yi mata katsalandan.

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP ya ci gaba da bayyana cewa makiya jihar marasu hankali ke bai wa gwamnatin tarayya shawarar daukar tsauraran matakai kan Jihar Kano ciki har da a kafa mata dokar ta-baci, inda ya sha alwashin cewa al’ummar Jihar Kano masu son zaman lafiya ne kuma ba za su bijire masa.

Kwankwaso ya kuma yi tsokaci kan yanayin siyasar da ke tunkara a zaben 2027, inda ya zargi wasu ‘yan siyasa na shirin tayar da tarzoma.

Ya sha alwashin cewa jam’iyyar NNPP ba za ta bari wadannan abubuwa su murkushe su ba, yana mai cewa, “Muna mai tabbatar wa duk wanda yake tunanin zai iya cin zarafinmu a siyasance, muna tabbatar da cewa a shirye muke mu yake shi.”

Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa ya gargadi gwamnatin tarayya da ta daina sauraron ‘yan siyasa marasa kishin kasa daga Kano, yana mai gargadin cewa irin wannan abu zai haifar da babban baraka.

“Kofarmu a bude take wajen tattaunawa, sulhu, da sasantawa, amma ba za mu amince da tsoratarwa da cin zarafin siyasa ba. Mun san yadda ake yin siyasa kuma za mu yi duk abin da ya dace domin kare kanmu daga duk wani sharri,” in ji Kwankwaso.

A hannu guda kuma, jam’iyyar APC reshen Jihar Kano ta yi kira a kama Kwankwaso.

A cikin wata sanarwa da shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Abdullahi Abbas ya fitar, ta ce jam’iyyar tana zargin Kwankwaso da haddasa tashin hankali kan zarge-zargen da yake yi wa gwamnatin tarayya.

Abbas ya bayyana cewa babu wata barazana da Kwankwaso zai yi wa gwamnatin tarayya.

“Jagoran jam’iyyar NNPP da ke fama da rikici wanda yake boye rashin aikin da gwamnatinsu ta kasa yi a cikin shekara daya da ta wuce, sannan kuma yana kokarin ganin ya mallaki siyasar Kano, ya kamata jami’an tsaro su kama shi domin ya bayyana wadanda ke daukar nauyin ‘yan ta’addan Boko Haram.

“Muna so mu yi kira ga jami’an tsaro da kakkausar murya da su kamo wannan mutumi domin ya bayyana sunayen wadanda ya kira makiyan Jihar Kano da ke yi wa gwamnatin tarayya aiki domin daukar nauyin ‘yan ta’addan Boko Haram da masu tayar da kayar baya,” in ji sanarwar.

Shugaban jam’iyyar ya yi nuni da cewa wadannan kalamai alama ce ta wata muguwar manufa da Kwankwaso da makarrabansa suka yi na kawo tashin hankali a Kano.

“Kwankwaso ya dade yana zama barazana ga Kano da kasa baki daya bisa la’akari da abubuwan da suka faru a baya. Yana gudanar da wata kungiyar asiri, inda ake zarginsa da daukar matasa aiki wanda akasarin su wadanda suka bar zuwa makaranta domin su tada zaune-tsaye a jihar.”

Abbas ya ce kafin zaben 2023 har ma lokacin zaben, an dauki dubbunnan matasa aiki domin tsoratar da jama’a ta hanyar kai musu hari da lalata dukiyoyin da ake ganin ‘yan adawa ne da kuma sace wayoyin mutane.

Shugaban jam’iyyar ya yi zargin cewa a lokacin da ake tafka shari’a kan zaben gwamna, Kwankwaso da mukarrabansa sun yi wa alkalai barazana.

Abbas ya ce tun bayan da aka maido da Alhaji Muhammadu Sanusi a matsayin sarki, an dauki daruruwan matasa aiki dauke da makamai tare da jibge su a fadar sarkin, lamarin da ke zama babbar barazana ga mazauna cikin fadar da kewaye.

Kano
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

An kashe Matashi Kan Batanci Ga Annabi A Jihar Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.