• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ce Ke Rura Wutar Rikici A Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Ce Ke Rura Wutar Rikici A Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu, sama da mutanen Palasdinu da na Isra’ila 7200 suka halaka, sakamakon rikicin da ya barke a tsakaninsu tun ranar 7 ga wata. Duk da haka, John Kirby, babban jami’in kwamitin kula da harkokin tsaro na fadar White House ya bayyana cewa, “lokaci bai yi da za a tsagaita bude wuta”, dole ne Hamas ta saki fursunonin da take tsare da su tukuna. Ya yi furucin ne a lokacin da yake tattaunawa da tashar CNN a ranar 23 ga wata, inda ya ce, “Akwai sauran ayyuka ga Isra’ila wajen farautar jagororin kungiyar Hamas…Mu kuma za mu mai da hankali a kan tabbatar musu da dukkanin abubuwan da suke bukata wajen fadan.” 

A yayin da rikici ke ci gaba da tabarbarewa tare da haifar da mutuwar dimbin fararen hula, tsagaita bude wuta abu ne da ya kamata a baiwa fifiko wajen tabbatar da shi, don haka ma galibin kasashen duniya na kira ga Palasdinu da Isra’ila da su dakatar da fada a tsakaninsu, amma ita kasar Amurka a maimakon haka, tana rura wutar rikicin, inda a kwanan nan, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya bukaci majalisar dokokin kasar da ta samar da dala biliyan 106, kuma daga cikin kudin, zai ware dala biliyan 14.3 ga Isra’ila a matsayin gudummawar soja. Baya ga haka, Amurka ta kuma tura jiragen ruwa masu daukar jiragen sama zuwa bahar Rum, tare da dada tura kayayyakin soja zuwa Isra’ila. Har ma sau biyu ne ta hana kwamitin sulhu na MDD zartas da daftarin kuduri da ya shafi batun Palasdinu da Isra’ila.

  • Me Ya Sa Dangantaka Da Sin Ke Samun Karbuwa A Afrika?
  • Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

Kwanan nan, shehun malami a jami’ar Harvard, Stephan Walt, ya rubuta a mujallar Foreign Policy cewa, “Amurka ita ce sanadin sabon rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila.” Abin haka yake, Amurka ta dade tana mai da Isra’ila a matsayin makaminta a gabas ta tsakiya, don haifar da barazana ga Iran da sauran kasashen yankin, a sa’i daya kuma, kasancewar Yahudawan kasar Amurka suna yawan samar da kudade ga babban zaben kasar Amurka, wadanda ke da muhimmin tasiri ga harkokin siyasa na Amurka, don haka ne gwamnatin kasar Amurka take ta nuna goyon baya ga Isra’ila a rikicinta da Palasdinu, matakin da ya sa aka dade ana fuskantar matsalar Palasdinu da Isra’ila.

Kwanan nan, shugaba Biden ya gabatar da jawabi a wani shirin talabijin, inda bai ko boye ba ya ce, nuna goyon baya ga muhimman kawayen Amurka da suka hada da Isra’ila da Ukraine “jari ne da aka zuba da idon basira, wanda zai haifar da alfanu ga zuriyoyin Amurka”. A game da haka, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha, Maria Zakharova ta ce, “Kullum yake-yake na kasance ‘jarin da Amurka ta zuba da idon basira’, kasancewar bai faru a yankin Amurka ba, don haka ma ba su damu da hasarorin da suka haifar ga sauran kasashe ba.”

Lallai Amurka ta sha zancen hakkin dan Adam, amma kuma ta kawar da ido daga masifar jin kai da ke faruwa a Gaza, Amurka wadda take daukar kanta a matsayin mai rajin kare dimokuradiyya da hakkin dan Adam, amma kuma tana dora moriyar kanta a kan ta sauran kasashe da ma dokokin kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Rikici na ci gaba a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wadda ke haifar da munanan hasarori ga fararen hula masu dimbin yawa. Sanyaya yanayin da ake ciki da ma magance hasarar rayukan fararen hula shi ne ainihin abin da ya kamata a yi wajen kare hakkin bil Adam. Kasashen duniya, musamman ma manyan kasashe, ya kamata su taka rawar da ta kamata, su dauki matakan da suka wajaba na sa kaimin yin shawarwari da dakatar da bude wuta, don maido da zaman lafiya tun da wuri.(Mai Zane: Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaFalasdinuIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Nada Kwamishinonin INEC A Jihohi 9

Next Post

Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

5 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

6 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

7 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

9 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

10 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

1 day ago
Next Post
Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.