• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ce Ke Rura Wutar Rikici A Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Ce Ke Rura Wutar Rikici A Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu, sama da mutanen Palasdinu da na Isra’ila 7200 suka halaka, sakamakon rikicin da ya barke a tsakaninsu tun ranar 7 ga wata. Duk da haka, John Kirby, babban jami’in kwamitin kula da harkokin tsaro na fadar White House ya bayyana cewa, “lokaci bai yi da za a tsagaita bude wuta”, dole ne Hamas ta saki fursunonin da take tsare da su tukuna. Ya yi furucin ne a lokacin da yake tattaunawa da tashar CNN a ranar 23 ga wata, inda ya ce, “Akwai sauran ayyuka ga Isra’ila wajen farautar jagororin kungiyar Hamas…Mu kuma za mu mai da hankali a kan tabbatar musu da dukkanin abubuwan da suke bukata wajen fadan.” 

A yayin da rikici ke ci gaba da tabarbarewa tare da haifar da mutuwar dimbin fararen hula, tsagaita bude wuta abu ne da ya kamata a baiwa fifiko wajen tabbatar da shi, don haka ma galibin kasashen duniya na kira ga Palasdinu da Isra’ila da su dakatar da fada a tsakaninsu, amma ita kasar Amurka a maimakon haka, tana rura wutar rikicin, inda a kwanan nan, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya bukaci majalisar dokokin kasar da ta samar da dala biliyan 106, kuma daga cikin kudin, zai ware dala biliyan 14.3 ga Isra’ila a matsayin gudummawar soja. Baya ga haka, Amurka ta kuma tura jiragen ruwa masu daukar jiragen sama zuwa bahar Rum, tare da dada tura kayayyakin soja zuwa Isra’ila. Har ma sau biyu ne ta hana kwamitin sulhu na MDD zartas da daftarin kuduri da ya shafi batun Palasdinu da Isra’ila.

  • Me Ya Sa Dangantaka Da Sin Ke Samun Karbuwa A Afrika?
  • Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

Kwanan nan, shehun malami a jami’ar Harvard, Stephan Walt, ya rubuta a mujallar Foreign Policy cewa, “Amurka ita ce sanadin sabon rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila.” Abin haka yake, Amurka ta dade tana mai da Isra’ila a matsayin makaminta a gabas ta tsakiya, don haifar da barazana ga Iran da sauran kasashen yankin, a sa’i daya kuma, kasancewar Yahudawan kasar Amurka suna yawan samar da kudade ga babban zaben kasar Amurka, wadanda ke da muhimmin tasiri ga harkokin siyasa na Amurka, don haka ne gwamnatin kasar Amurka take ta nuna goyon baya ga Isra’ila a rikicinta da Palasdinu, matakin da ya sa aka dade ana fuskantar matsalar Palasdinu da Isra’ila.

Kwanan nan, shugaba Biden ya gabatar da jawabi a wani shirin talabijin, inda bai ko boye ba ya ce, nuna goyon baya ga muhimman kawayen Amurka da suka hada da Isra’ila da Ukraine “jari ne da aka zuba da idon basira, wanda zai haifar da alfanu ga zuriyoyin Amurka”. A game da haka, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha, Maria Zakharova ta ce, “Kullum yake-yake na kasance ‘jarin da Amurka ta zuba da idon basira’, kasancewar bai faru a yankin Amurka ba, don haka ma ba su damu da hasarorin da suka haifar ga sauran kasashe ba.”

Lallai Amurka ta sha zancen hakkin dan Adam, amma kuma ta kawar da ido daga masifar jin kai da ke faruwa a Gaza, Amurka wadda take daukar kanta a matsayin mai rajin kare dimokuradiyya da hakkin dan Adam, amma kuma tana dora moriyar kanta a kan ta sauran kasashe da ma dokokin kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Rikici na ci gaba a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wadda ke haifar da munanan hasarori ga fararen hula masu dimbin yawa. Sanyaya yanayin da ake ciki da ma magance hasarar rayukan fararen hula shi ne ainihin abin da ya kamata a yi wajen kare hakkin bil Adam. Kasashen duniya, musamman ma manyan kasashe, ya kamata su taka rawar da ta kamata, su dauki matakan da suka wajaba na sa kaimin yin shawarwari da dakatar da bude wuta, don maido da zaman lafiya tun da wuri.(Mai Zane: Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaFalasdinuIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Nada Kwamishinonin INEC A Jihohi 9

Next Post

Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

Related

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

18 hours ago
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
Daga Birnin Sin

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

19 hours ago
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

20 hours ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

21 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

22 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

23 hours ago
Next Post
Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.