ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ce Ke Rura Wutar Rikici A Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila

by CGTN Hausa
3 years ago
Amurka

Kawo yanzu, sama da mutanen Palasdinu da na Isra’ila 7200 suka halaka, sakamakon rikicin da ya barke a tsakaninsu tun ranar 7 ga wata. Duk da haka, John Kirby, babban jami’in kwamitin kula da harkokin tsaro na fadar White House ya bayyana cewa, “lokaci bai yi da za a tsagaita bude wuta”, dole ne Hamas ta saki fursunonin da take tsare da su tukuna. Ya yi furucin ne a lokacin da yake tattaunawa da tashar CNN a ranar 23 ga wata, inda ya ce, “Akwai sauran ayyuka ga Isra’ila wajen farautar jagororin kungiyar Hamas…Mu kuma za mu mai da hankali a kan tabbatar musu da dukkanin abubuwan da suke bukata wajen fadan.” 

A yayin da rikici ke ci gaba da tabarbarewa tare da haifar da mutuwar dimbin fararen hula, tsagaita bude wuta abu ne da ya kamata a baiwa fifiko wajen tabbatar da shi, don haka ma galibin kasashen duniya na kira ga Palasdinu da Isra’ila da su dakatar da fada a tsakaninsu, amma ita kasar Amurka a maimakon haka, tana rura wutar rikicin, inda a kwanan nan, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya bukaci majalisar dokokin kasar da ta samar da dala biliyan 106, kuma daga cikin kudin, zai ware dala biliyan 14.3 ga Isra’ila a matsayin gudummawar soja. Baya ga haka, Amurka ta kuma tura jiragen ruwa masu daukar jiragen sama zuwa bahar Rum, tare da dada tura kayayyakin soja zuwa Isra’ila. Har ma sau biyu ne ta hana kwamitin sulhu na MDD zartas da daftarin kuduri da ya shafi batun Palasdinu da Isra’ila.

  • Me Ya Sa Dangantaka Da Sin Ke Samun Karbuwa A Afrika?
  • Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

Kwanan nan, shehun malami a jami’ar Harvard, Stephan Walt, ya rubuta a mujallar Foreign Policy cewa, “Amurka ita ce sanadin sabon rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila.” Abin haka yake, Amurka ta dade tana mai da Isra’ila a matsayin makaminta a gabas ta tsakiya, don haifar da barazana ga Iran da sauran kasashen yankin, a sa’i daya kuma, kasancewar Yahudawan kasar Amurka suna yawan samar da kudade ga babban zaben kasar Amurka, wadanda ke da muhimmin tasiri ga harkokin siyasa na Amurka, don haka ne gwamnatin kasar Amurka take ta nuna goyon baya ga Isra’ila a rikicinta da Palasdinu, matakin da ya sa aka dade ana fuskantar matsalar Palasdinu da Isra’ila.

ADVERTISEMENT

Kwanan nan, shugaba Biden ya gabatar da jawabi a wani shirin talabijin, inda bai ko boye ba ya ce, nuna goyon baya ga muhimman kawayen Amurka da suka hada da Isra’ila da Ukraine “jari ne da aka zuba da idon basira, wanda zai haifar da alfanu ga zuriyoyin Amurka”. A game da haka, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha, Maria Zakharova ta ce, “Kullum yake-yake na kasance ‘jarin da Amurka ta zuba da idon basira’, kasancewar bai faru a yankin Amurka ba, don haka ma ba su damu da hasarorin da suka haifar ga sauran kasashe ba.”

Lallai Amurka ta sha zancen hakkin dan Adam, amma kuma ta kawar da ido daga masifar jin kai da ke faruwa a Gaza, Amurka wadda take daukar kanta a matsayin mai rajin kare dimokuradiyya da hakkin dan Adam, amma kuma tana dora moriyar kanta a kan ta sauran kasashe da ma dokokin kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Rikici na ci gaba a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wadda ke haifar da munanan hasarori ga fararen hula masu dimbin yawa. Sanyaya yanayin da ake ciki da ma magance hasarar rayukan fararen hula shi ne ainihin abin da ya kamata a yi wajen kare hakkin bil Adam. Kasashen duniya, musamman ma manyan kasashe, ya kamata su taka rawar da ta kamata, su dauki matakan da suka wajaba na sa kaimin yin shawarwari da dakatar da bude wuta, don maido da zaman lafiya tun da wuri.(Mai Zane: Mustapha Bulama)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.