• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Wadda Ke Tayar Da Yake-Yake A Duniya Ta Haifar Da Rikicin ’Yan Gudun Hijira

byCMG Hausa
2 years ago
Amurka

Yau, ranar ’yan gudun hijira ce ta kasa da kasa. Na zana wani yaro mai suna Alan Kurdi, mai shekaru 3 kacal a duniya, ya mutu kan hanyarsa ta gudun hijira, bayan da ya rasa gidansu sanadiyyar yaki a kasar Sham.

Amma, bakin ciki shi ne, a kullum ana samun yara irinsu Alan Kurdi dake rasa rayukansu saboda yake-yake. Alkaluman kididdiga da hukumar kula da kaurar jama’a ta kasa da kasa ta fitar na nuna cewa, tun daga shekarar 2014, yawan ’yan kasar Sham dake gudun hijira, kuma suka mutu a kan hanyarsu ta neman tsira ya haura dubu 29. Baya ga miliyan 5.4 dake gudun hijira a wasu kasashe, yayin da wasu miliyan 13.5 kuma ke matukar bukatar tallafin jin kai.

  • Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

A halin yanzu, kashi 72% na ’yan gudun hijira a duniya, sun fito ne daga kasashen Sham da Venezuela da Ukraine da Afghanistan da Sudan ta kudu. Rikicin ’yan gudun hijira da wadannan kasashe suke fuskanta na da alaka sosai da Amurka, saboda tsoma baki a harkokin cikin gidan kasashen da kuma amfani da karfin tuwo da gwamnatin Amurka take yi. MDD ta ba da alkaluma cewa, tun barkewar yakin Sham a shekarar 2011, matakan soja da Amurka ta dauka a Sham, sun haifar da mutuwar mutane a kalla dubu 350, yayin da rabin al’ummar kasar ke gudun hijira, ga matsalar gidaje da ta abinci, abin da ya zama rikicin jin kai mafi tsananni tun lokacin da aka kawo karshen yakin duniya na biyu.

An dauki hoton Alan Kurdi wanda ya mutu a gabar teku a shekarar 2015, abin da ya girgiza duk duniya baki daya, tare da sosan ran mutane. Amma ’yan siyasa na Amurka sun nuna halin ko-in-kula, suna ci gaba da daukar matakin soja a duniya. Amurka mai haifar da rikicin ’yan gudun hijira, ba ta kula da hakkin bil Adama, sai moriyar siyasa kawai. Muna fatan a dakatar da yake-yake a duniya, don ceton rayukan kananan yara kamar Alan Kurdi.

Amma wannan fata ba zai taba tabbata a duniya ba, sai ’yan siyasar Amurka sun yi watsi da moriyar kashin kai, sun yi la’akari da hakkin bil Adama, musamman ma hakkin kare rayukan kananan yara a duniya. (Mai zana da rubuta: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Gwamnan Bauchi Ya Sake Nada Gidado A Matsayin Mashawarci Kan Yada Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sake Nada Gidado A Matsayin Mashawarci Kan Yada Labarai

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version