• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ƙaddamar Da Cibiyar Ƴan Jarida Ta Afrika Masu Amfani Da Harshen Hausa A Nijar

by Muhammad Bashir
10 months ago
in Al'adu, Kasashen Ketare, Labarai
0
Daga Hagu zuwa Dama 1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya 2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar 3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey 4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan'jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa 5. Mamman Idi Liman 6. Barau Tandja

Daga Hagu zuwa Dama 1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya 2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar 3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey 4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan'jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa 5. Mamman Idi Liman 6. Barau Tandja

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙoƙarin da ake na bunƙasa ayyukan yan jarida masu amfani da harshen hausa a Nahiyar Afrika, an ƙaddamar da cibiyar ƙungiyar a birnin Niamey na Jamhuriyar Nijar.

Wannan ne karo na farko da aka samar da irin wannan ƙungiya bisa la’akari da jajircewar da ake yi na ganin an bunƙasa harsunan cikin gida musamman Hausa, wanda yake ƙoƙarin mamaye sauran harsuna a nahiyar Afrika.

  • Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda
  • Mataimakin Shugaban Sin Ya Gana Da Firaministan Jamhuriyar Nijar

A yayin ƙaddamar da cibiyar ƙungiyar tare da kwarkwaryar zantawa da yan jaridu na ƙasa da ƙasa, da sauran wakilai da suka zo daga sassa daban daban ciki har da Nijeriya, masu ruwa da tsaki a wannan taro sun bayyana muhimmancin wannan ƙungiya wadda take da manufar aiwatar da aikin jarida nagartacce musamman zaburar da jama’a akan muhimmancin gina al’umma da samar da ci gaba mai ɗorewa.

Maryam Sarki Azbin wadda ta zama jigo wajen samar da wannan ƙungiya tace lokaci ya yi da za a riƙa amfani da harshen cikin gida wajen isar da muhimman saƙonni ga al’umma a duk inda suke.

Sarki Azbin ta bukaci yan jarida dasu kaucewa abubuwan da suke ɓata wa aikinsu kima a idon jama’a kamar izgilanci, da maula, da kwaɗayi, da banbaɗanci da keta mutuncin masu faɗa a ji.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

Ta ƙara da cewa, ƙungiyar ta yan’jarida zata yi dukkan mai yiwa wajen zaburar da yan jaridu akan yadda zasu rika amfani da harshen Hausa wajen sanar da mutane abubuwan da zasu amfane su a rayuwarsu ta yau da kullum.

A jawabinsa, shugaban hukumar gidan telebijin da radiyo na jamhuriyar Niger, RTN, Abdoulaye Koulibaly ya bayyana cewa aikin jarida aiki ne da yake buƙatar gaskiya da sanin makamar aiki, a don haka kuskure ne yan jarida suke yi wajen bada labarai na shaci-faɗi don son abin hannu wasu masu faɗa a ji, ko kuma nuna bangaranci yayin fitar da labarai.

Daga Hagu zuwa Dama1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya 2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar 3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey 4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan'jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa 5. Mamman Idi Liman 6. Barau Tandja
Daga Hagu zuwa Dama
1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya
2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar
3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey
4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan’jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa
5. Mamman Idi Liman
6. Barau Tandja

Koulibali yace samar da wannan ƙungiya wata dama ce da zata taimaka wajen magance ƙalubalen da yan jarida suke fuskanta ta fannin gudanar da ayyukansu musamman wajen amfani da harshe na cikin gida.

Sauran waɗanda suka yi jawabi a wurin sun gamsu da tsare-tsare da manufofin da aka gina ƙungiyar akan su musamman tabbatar da hadin kai da mu’amala a tsakanin yan jarida na ƙasashe 11 dake Nahiyar Afrika suna masu cewa yawan da yan jaridar Hausa da ake da su a Nahiyar, sun isa su taka gagarumar gudunmawa wajen magance ƙalubalen da ake fuskanta, da kuma ƙarfafawa masu madafun iko gwuiwa wajen ganin sun yi abin da ya dace na kyautata rayuwar al’ummar yankin.

Aliyu Rabe Aliyu Ma’aikaci a hukumar Telebijin a tarayyar Nijeriya (NTA), ya ce, babban aikin da ƙungiyar ƴan jarida masu amfani da harshen Hausa za ta sa a gaba shi ne sauya fasalin aikin jaridar gado na ‘yan ku ci ku bamu, ya zuwa aikin jarida na samar da mafita ga tulin ƙalubalen da yankin yake fuskanta ta hanyar amfani da harshen da kowa yake sonsa, kuma yake amfani da shi watau harshen HAUSA.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HausaJaridaNijarNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ɗaliban Cyprus: Zamfara Ta Samar Wa Ɗalibanta ‘Yanci Da Ke Karatu A Gida Da Ƙetare

Next Post

Shugabannin Kasashen Waje Za Su Halarci CIIE Karo Na 7

Related

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

28 minutes ago
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

1 hour ago
An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi
Labarai

An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

2 hours ago
An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina
Labarai

An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

3 hours ago
Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1
Labarai

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

4 hours ago
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

5 hours ago
Next Post
Shugabannin Kasashen Waje Za Su Halarci CIIE Karo Na 7

Shugabannin Kasashen Waje Za Su Halarci CIIE Karo Na 7

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

September 4, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

September 4, 2025
An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

September 4, 2025
An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

September 4, 2025
Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

September 4, 2025
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

September 4, 2025
Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

September 4, 2025
Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.