ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ƙaddamar Da Cibiyar Ƴan Jarida Ta Afrika Masu Amfani Da Harshen Hausa A Nijar

by Muhammad Bashir
1 year ago
Daga Hagu zuwa Dama 1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya 2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar 3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey 4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan'jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa 5. Mamman Idi Liman 6. Barau Tandja

Daga Hagu zuwa Dama 1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya 2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar 3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey 4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan'jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa 5. Mamman Idi Liman 6. Barau Tandja

A ƙoƙarin da ake na bunƙasa ayyukan yan jarida masu amfani da harshen hausa a Nahiyar Afrika, an ƙaddamar da cibiyar ƙungiyar a birnin Niamey na Jamhuriyar Nijar.

Wannan ne karo na farko da aka samar da irin wannan ƙungiya bisa la’akari da jajircewar da ake yi na ganin an bunƙasa harsunan cikin gida musamman Hausa, wanda yake ƙoƙarin mamaye sauran harsuna a nahiyar Afrika.

  • Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda
  • Mataimakin Shugaban Sin Ya Gana Da Firaministan Jamhuriyar Nijar

A yayin ƙaddamar da cibiyar ƙungiyar tare da kwarkwaryar zantawa da yan jaridu na ƙasa da ƙasa, da sauran wakilai da suka zo daga sassa daban daban ciki har da Nijeriya, masu ruwa da tsaki a wannan taro sun bayyana muhimmancin wannan ƙungiya wadda take da manufar aiwatar da aikin jarida nagartacce musamman zaburar da jama’a akan muhimmancin gina al’umma da samar da ci gaba mai ɗorewa.

ADVERTISEMENT

Maryam Sarki Azbin wadda ta zama jigo wajen samar da wannan ƙungiya tace lokaci ya yi da za a riƙa amfani da harshen cikin gida wajen isar da muhimman saƙonni ga al’umma a duk inda suke.

Sarki Azbin ta bukaci yan jarida dasu kaucewa abubuwan da suke ɓata wa aikinsu kima a idon jama’a kamar izgilanci, da maula, da kwaɗayi, da banbaɗanci da keta mutuncin masu faɗa a ji.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Ta ƙara da cewa, ƙungiyar ta yan’jarida zata yi dukkan mai yiwa wajen zaburar da yan jaridu akan yadda zasu rika amfani da harshen Hausa wajen sanar da mutane abubuwan da zasu amfane su a rayuwarsu ta yau da kullum.

A jawabinsa, shugaban hukumar gidan telebijin da radiyo na jamhuriyar Niger, RTN, Abdoulaye Koulibaly ya bayyana cewa aikin jarida aiki ne da yake buƙatar gaskiya da sanin makamar aiki, a don haka kuskure ne yan jarida suke yi wajen bada labarai na shaci-faɗi don son abin hannu wasu masu faɗa a ji, ko kuma nuna bangaranci yayin fitar da labarai.

Daga Hagu zuwa Dama1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya 2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar 3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey 4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan'jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa 5. Mamman Idi Liman 6. Barau Tandja
Daga Hagu zuwa Dama
1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya
2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar
3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey
4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan’jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa
5. Mamman Idi Liman
6. Barau Tandja

Koulibali yace samar da wannan ƙungiya wata dama ce da zata taimaka wajen magance ƙalubalen da yan jarida suke fuskanta ta fannin gudanar da ayyukansu musamman wajen amfani da harshe na cikin gida.

Sauran waɗanda suka yi jawabi a wurin sun gamsu da tsare-tsare da manufofin da aka gina ƙungiyar akan su musamman tabbatar da hadin kai da mu’amala a tsakanin yan jarida na ƙasashe 11 dake Nahiyar Afrika suna masu cewa yawan da yan jaridar Hausa da ake da su a Nahiyar, sun isa su taka gagarumar gudunmawa wajen magance ƙalubalen da ake fuskanta, da kuma ƙarfafawa masu madafun iko gwuiwa wajen ganin sun yi abin da ya dace na kyautata rayuwar al’ummar yankin.

Aliyu Rabe Aliyu Ma’aikaci a hukumar Telebijin a tarayyar Nijeriya (NTA), ya ce, babban aikin da ƙungiyar ƴan jarida masu amfani da harshen Hausa za ta sa a gaba shi ne sauya fasalin aikin jaridar gado na ‘yan ku ci ku bamu, ya zuwa aikin jarida na samar da mafita ga tulin ƙalubalen da yankin yake fuskanta ta hanyar amfani da harshen da kowa yake sonsa, kuma yake amfani da shi watau harshen HAUSA.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Shugabannin Kasashen Waje Za Su Halarci CIIE Karo Na 7

Shugabannin Kasashen Waje Za Su Halarci CIIE Karo Na 7

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.