ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ƙaddamar Da Cibiyar Ƴan Jarida Ta Afrika Masu Amfani Da Harshen Hausa A Nijar

by Muhammad Bashir
2 years ago
Daga Hagu zuwa Dama 1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya 2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar 3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey 4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan'jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa 5. Mamman Idi Liman 6. Barau Tandja

Daga Hagu zuwa Dama 1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya 2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar 3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey 4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan'jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa 5. Mamman Idi Liman 6. Barau Tandja

A ƙoƙarin da ake na bunƙasa ayyukan yan jarida masu amfani da harshen hausa a Nahiyar Afrika, an ƙaddamar da cibiyar ƙungiyar a birnin Niamey na Jamhuriyar Nijar.

Wannan ne karo na farko da aka samar da irin wannan ƙungiya bisa la’akari da jajircewar da ake yi na ganin an bunƙasa harsunan cikin gida musamman Hausa, wanda yake ƙoƙarin mamaye sauran harsuna a nahiyar Afrika.

  • Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda
  • Mataimakin Shugaban Sin Ya Gana Da Firaministan Jamhuriyar Nijar

A yayin ƙaddamar da cibiyar ƙungiyar tare da kwarkwaryar zantawa da yan jaridu na ƙasa da ƙasa, da sauran wakilai da suka zo daga sassa daban daban ciki har da Nijeriya, masu ruwa da tsaki a wannan taro sun bayyana muhimmancin wannan ƙungiya wadda take da manufar aiwatar da aikin jarida nagartacce musamman zaburar da jama’a akan muhimmancin gina al’umma da samar da ci gaba mai ɗorewa.

ADVERTISEMENT

Maryam Sarki Azbin wadda ta zama jigo wajen samar da wannan ƙungiya tace lokaci ya yi da za a riƙa amfani da harshen cikin gida wajen isar da muhimman saƙonni ga al’umma a duk inda suke.

Sarki Azbin ta bukaci yan jarida dasu kaucewa abubuwan da suke ɓata wa aikinsu kima a idon jama’a kamar izgilanci, da maula, da kwaɗayi, da banbaɗanci da keta mutuncin masu faɗa a ji.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Ta ƙara da cewa, ƙungiyar ta yan’jarida zata yi dukkan mai yiwa wajen zaburar da yan jaridu akan yadda zasu rika amfani da harshen Hausa wajen sanar da mutane abubuwan da zasu amfane su a rayuwarsu ta yau da kullum.

A jawabinsa, shugaban hukumar gidan telebijin da radiyo na jamhuriyar Niger, RTN, Abdoulaye Koulibaly ya bayyana cewa aikin jarida aiki ne da yake buƙatar gaskiya da sanin makamar aiki, a don haka kuskure ne yan jarida suke yi wajen bada labarai na shaci-faɗi don son abin hannu wasu masu faɗa a ji, ko kuma nuna bangaranci yayin fitar da labarai.

Daga Hagu zuwa Dama1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya 2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar 3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey 4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan'jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa 5. Mamman Idi Liman 6. Barau Tandja
Daga Hagu zuwa Dama
1. Aliyu Rabe Aliyu NTA, Nijeriya
2. Abdullaye Koulibaley: Shugaban Hukumar Radio da Telebijin Na Jamhuriyar Nijar
3. Guimbe Kochi Ragiou; Magatakardan Gwamnan Birnin Niamey
4. Hajiya Mariam Lawali Sarki Azbin; Shugabar Kungiyar Yan’jarida Na Afrika masu amfani da Harshen Hausa
5. Mamman Idi Liman
6. Barau Tandja

Koulibali yace samar da wannan ƙungiya wata dama ce da zata taimaka wajen magance ƙalubalen da yan jarida suke fuskanta ta fannin gudanar da ayyukansu musamman wajen amfani da harshe na cikin gida.

Sauran waɗanda suka yi jawabi a wurin sun gamsu da tsare-tsare da manufofin da aka gina ƙungiyar akan su musamman tabbatar da hadin kai da mu’amala a tsakanin yan jarida na ƙasashe 11 dake Nahiyar Afrika suna masu cewa yawan da yan jaridar Hausa da ake da su a Nahiyar, sun isa su taka gagarumar gudunmawa wajen magance ƙalubalen da ake fuskanta, da kuma ƙarfafawa masu madafun iko gwuiwa wajen ganin sun yi abin da ya dace na kyautata rayuwar al’ummar yankin.

Aliyu Rabe Aliyu Ma’aikaci a hukumar Telebijin a tarayyar Nijeriya (NTA), ya ce, babban aikin da ƙungiyar ƴan jarida masu amfani da harshen Hausa za ta sa a gaba shi ne sauya fasalin aikin jaridar gado na ‘yan ku ci ku bamu, ya zuwa aikin jarida na samar da mafita ga tulin ƙalubalen da yankin yake fuskanta ta hanyar amfani da harshen da kowa yake sonsa, kuma yake amfani da shi watau harshen HAUSA.

Nijar
Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025

MASU ALAKA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
Labarai

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
Labarai

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Labarai

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Next Post
Shugabannin Kasashen Waje Za Su Halarci CIIE Karo Na 7

Shugabannin Kasashen Waje Za Su Halarci CIIE Karo Na 7

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.