• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ɗage Shari’ar Da Gwamnatin Kano Ta Kai Karar Aminu Ado Bayero Zuwa 2 Ga Watan Yuli

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Kano

Wata babbar kotun jihar Kano ta ɗage sauraren ƙarar da gwamnatin jihar Kano ta shigar a kan Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero da wasu sarakuna huɗu zuwa ranar 2 ga Yuli, 2024. Shari’ar na neman hana su gabatar da kansu a matsayin Sarakuna.

Mai shari’a Amina Adamu Aliyu, ta saurari kowanne ɓangare biyun, ciki har da lauyan Aminu Ado, Barr. Ibrahim Muktar, da kuma na gwamnatin jihar Kano, Barr. Ibrahim Isah-Wangida.

  • Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir
  • Rikicin Masarautar Kano: An Tura Ƙarin ‘Yansanda Fadar Ƙofar Kudu Da Gidan Nassarawa

Kotun dai ta shirya yin hukunci ne kan wata buƙata gami da umarnin shiga tsakani biyo bayan umarnin wucin gadi da aka bayar a baya.

Sai dai lauyoyin Aminu Ado sun shigar da wata sabuwar buƙatar a gaban kotu, inda suka bukaci ƙarin shigar da wasu cikin waɗanda ya kamata su bayar da jawabi. Sun haɗa da; ragowar sarakuna da hukumomin tsaro.

A baya dai, yunƙurin kai wa waɗanda ake ƙara takardar gayyata ya samu cikas, bayan da wata babbar kotun tarayya ta bayar da umarnin hana cin zarafi da tsoratarwa, kamar yadda Abdulsalam Saleh, lauyan Sufeto Janar na ‘yan sanda (IGP) ta bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Mai shari’a Amina Adamu ta ba da umarnin a bi ta hannun kwamishinan Ƴansandan jihar Kano wajen isar da ita gayyatar, tare da sanya ranar 24 ga watan Yunin 2024 a matsayin ranar ci gaba da sauraron ƙarar.

A yayin ci gaba da shari’ar, lauyan Aminu Ado ya buƙaci a yi watsi da ƙarar, yana mai bayar da hujjar rashin hurumin kotun. Amma lauyan gwamnati ya tabbatar da hurumin kotun kuma ya buƙaci a ci gaba da sauraren karar.

Mai shari’a Amina Adamu ta ɗage sauraron karar zuwa ranar 2 ga watan Yuli, 2024, domin ci gaba da tattaunawa kan waɗannan batutuwa da kuma ci gaba da shari’a. ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 2 ga watan Yuli, 2024, domin ci gaba da tattaunawa kan waɗannan batutuwa da kuma ci gaba da shari’a.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Next Post
Sabon Kwamishinan Ƴansandan Kano Ya Kama Aiki

Sabon Kwamishinan Ƴansandan Kano Ya Kama Aiki

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.