• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ɗage Shari’ar Da Gwamnatin Kano Ta Kai Karar Aminu Ado Bayero Zuwa 2 Ga Watan Yuli

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
An Ɗage Shari’ar Da Gwamnatin Kano Ta Kai Karar Aminu Ado Bayero Zuwa 2 Ga Watan Yuli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun jihar Kano ta ɗage sauraren ƙarar da gwamnatin jihar Kano ta shigar a kan Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero da wasu sarakuna huɗu zuwa ranar 2 ga Yuli, 2024. Shari’ar na neman hana su gabatar da kansu a matsayin Sarakuna.

Mai shari’a Amina Adamu Aliyu, ta saurari kowanne ɓangare biyun, ciki har da lauyan Aminu Ado, Barr. Ibrahim Muktar, da kuma na gwamnatin jihar Kano, Barr. Ibrahim Isah-Wangida.

  • Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir
  • Rikicin Masarautar Kano: An Tura Ƙarin ‘Yansanda Fadar Ƙofar Kudu Da Gidan Nassarawa

Kotun dai ta shirya yin hukunci ne kan wata buƙata gami da umarnin shiga tsakani biyo bayan umarnin wucin gadi da aka bayar a baya.

Sai dai lauyoyin Aminu Ado sun shigar da wata sabuwar buƙatar a gaban kotu, inda suka bukaci ƙarin shigar da wasu cikin waɗanda ya kamata su bayar da jawabi. Sun haɗa da; ragowar sarakuna da hukumomin tsaro.

A baya dai, yunƙurin kai wa waɗanda ake ƙara takardar gayyata ya samu cikas, bayan da wata babbar kotun tarayya ta bayar da umarnin hana cin zarafi da tsoratarwa, kamar yadda Abdulsalam Saleh, lauyan Sufeto Janar na ‘yan sanda (IGP) ta bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Mai shari’a Amina Adamu ta ba da umarnin a bi ta hannun kwamishinan Ƴansandan jihar Kano wajen isar da ita gayyatar, tare da sanya ranar 24 ga watan Yunin 2024 a matsayin ranar ci gaba da sauraron ƙarar.

A yayin ci gaba da shari’ar, lauyan Aminu Ado ya buƙaci a yi watsi da ƙarar, yana mai bayar da hujjar rashin hurumin kotun. Amma lauyan gwamnati ya tabbatar da hurumin kotun kuma ya buƙaci a ci gaba da sauraren karar.

Mai shari’a Amina Adamu ta ɗage sauraron karar zuwa ranar 2 ga watan Yuli, 2024, domin ci gaba da tattaunawa kan waɗannan batutuwa da kuma ci gaba da shari’a. ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 2 ga watan Yuli, 2024, domin ci gaba da tattaunawa kan waɗannan batutuwa da kuma ci gaba da shari’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AKYAminu Ado BayerokanoSunusi Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Masarautar Kano: An Tura Ƙarin ‘Yansanda Fadar Ƙofar Kudu Da Gidan Nassarawa

Next Post

Sabon Kwamishinan Ƴansandan Kano Ya Kama Aiki

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

2 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

4 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

18 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

18 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

19 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

20 hours ago
Next Post
Sabon Kwamishinan Ƴansandan Kano Ya Kama Aiki

Sabon Kwamishinan Ƴansandan Kano Ya Kama Aiki

LABARAI MASU NASABA

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.