ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir

by Abubakar Abba
2 years ago
Kano

Wata gidauniyar shirin ‘ya’yan Itatuwa da ke gudanar da aikinta a Nijeriya, wato (HortiNigeria), ta wanzar da wani shiri nata na yakar cutar da ke lalata Tumatirin da manoma suka shuka, wanda a turance ake kira da suna ‘Tuta Absoluta’.

Gidauniyar ta wanzar da shirin ne a Jihohin Kano, Kaduna da kuma a sauran wasu jihohi uku, a karkashin shirin aikin noma na Kasar Jamus.

  • Yau Kotun Tarayya Za Ta Yanke Hukuncin Masarautar Kano
  • Daga Kai Kuɗin Fansa ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shi A Dajin Kachiya

Har ila yau, ta yi hakan ne; domin sama wa manoma kayan aikin da za su yaki wannan cuta da ta jima shekara da shekaru tana addabar Tumatirin da manoma suka shuka.

ADVERTISEMENT

Kazalika, Gidauniyar ta wanzar da wannan aikin ne ta hanyar yin hadaka da wasu masu ruwa da tsaki a wadannan jihohi da abin ya shafa.

A karkashin hadakar, manoma Tumatirin kimanin 60,000 ne za su amfana da sabbin kayan aikin na zamani, domin yakar cutar ta mai suna ‘Tuta absoluta’ a Jihohin Kano da Kaduna da kuma sauran wasu jihohi uku.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Jagoran aikin tare da fadakarwa na Gidauniyar, Malam Abdullahi Umar ya sanar da hakan ne a yayin taron wayar da kan manoman Tumatirin, wanda Gidanuniyar ta gudanar a gonakin wasu daga cikin manoman da cutar ta bulla a bangaren nasu.

Haka zalika, Gidauniyar ta yi taron ne a karkashin wani aikinta na kare kwarin da ke yi wa Tumatir din da aka shuka illa, wato (IPM).

A cewar Abdullahi, “Manoma Tumatirin sama da 60,000 da ke Jihohin Kano da Kaduna sauran wasu jihohi ne muke sa ran za su amfana da kayan aikin na zamani”.

Ya ci gaba da cewa, a karkashin aikin za a horar da manoma a yankuna daban-daban da ke fadin jihar.

“Mun jima muna karfafa wa manoman Tumatir gwiwa, musamman a kan cewa kada su sake su gaza wajen ci gaba da yin wannan noma na Tumatir, sakamakon bullar wannan cuta; domin kuwa muna da yakinin cewa; akwai yadda za a yi a iya magance cutar ba da jimawa ba, da yardar Allah”.

Kazalika, ya kuma sake bayyana cewa; muna nan muna ci gaba da kokarin sama wa wadannan manoman na Tumatir kasuwa, yadda za su rika sayar da shi cikin sauki tare kuma da samun kudaden shiga a cikin aljihunansu.

Shi ma a nasa bangaren, wani kwararre a cikin aikin; Mista Sabastine Agada Obaje ya yi nuni da cewa, yin gwajin na da matukar mahimmanci, domin kuwa ta hanyar yin gwajin ne za a iya taimaka wa manoman yin amfani da dabarun fasahar zamani wajen yin wannan noma na Tumatir.

Guda daga cikin manoman Tumatirin, Malam Uba Bello a nasa jawabin a wajen gwajin ya bayyana cewa, taron ya kara wa manoman Tumatirin kwarin gwaiwa, kan yadda za su tunkari kalubalen bullar cutar a gonakinsu.

A cewar tasa, sabuwar fasahar zamanin; tabbas za ta taimaka wa manoman Tumatir, kan yadda za su kara habaka sana’arsu ta wannan noma na Tumatir.

Ya kara da cewa, hakan zai kuma bai wa sauran manoman; musamman wadanda cutar ta sa suka dakatar da yin noman Timatirin samun damar dawowa cikin sana’ar gadan-gadan.

Kano
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.