• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ɗaure Mutum 14 Kan Yaɗa Bidiyon Maɗigo A Jamhuriyar Nijar

byMuhammad
3 years ago

Kotu a birnin Maradi da ke Jamhuriyar Nijar ta yanke wa wasu matasa hukuncin ɗaurin shekara uku-uku a gidan yari, bayan samunsu da laifin naɗa da kuma yaɗa wani bidiyo da ke nuna wasu mata biyu suna madigo.

BBC ta rawaito cewa, wadanda aka yanke wa hukuncin sun haɗa da mata 13 da namiji ɗaya.

  • ‘Ƴar Majalisa Na Burin A Samar Da Tsauraran Dokoki Kan ‘Yan Luwadi Da Madigo A Nijar
  • Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane Fiye Da 130 Cikin Wata Biyu A Nijar

Baya ga hukuncin ɗaurin, kotun ta ci tarar matan su 13 Sefa miliyan ɗaya kowace yayin da aka ci namijin tarar sefa miliyan uku kasancewarsa wanda ke da dandalin manhajar Whatsapp din da aka yadda wannan bidiyon.

Makonni biyu da suka wuce ne dai aka fara gurfanar da mutanen 14 gaban kotun bisa zarginsu da aikata laifin yaɗa abu ta shafukan intanet da ka iya tayar da hankalin jama’a.

Laifin, a cewar lauya mai shigar da ƙara ya saɓawa dokar haramta aikata laifuka ta shafukan intanet.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Ya kuma nemi a yi mu su hukunci mafi tsanani na ɗaurin shekaru uku; wanda kuma shi ne kotun ta sanar a ranar Alhamis.

Jami’an tsaro na jandarma ne suka kakkama matasa bayan wani koke da wasu mutane suka yi kan yaɗa bidiyon na batsa.

Dukansu dai an same su da laifin yaɗa abubuwan batsa da nuna tsiraicin ɗan adama da kuma tayar wa jama’a hankali.

Sai dai kotun ta ba su damar ɗaukaka ƙara a cikin kwana 10, kamar yadda dokokin ƙasar suka tanada.

Wannan shari’ar dai ta ja hankalin mutane a ciki da wajen ƙasar ta Nijar saboda yadda aka ce a farkon shari’ar aka yi ta muhawara kan wace doka za a yi amfani da ita wajen yi musu shari’a.

Hakan ya faru ne kasancewar dokokin ba su tanadi hukunci ƙarara da za a iya yankewa wadanda aka samu da aikata laifin luwaɗi ko maɗigo ba.

Ba mamaki wannan ne ya sa aka yi amfani da dokar haramta yaɗa abubuwa masu tayar da hankali a shafukan inta wajen yi musu shari’a.

Sakamakon haka dai yanzu haka wata ƴar majalisar dokokin ƙasar ta gabatar da ƙuduri gaban majalisar da ke neman yin dokar haramta luwadi da maɗigo a ƙasar mai rinjayen Musulmi da ke yammacin Afrika.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa - Sarkin Zazzau

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version