ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

by Sadiq
4 years ago
Sarkin Zazzau

Mai martaba Sarkin Zazzau kuma babban mataimaki na kungiyar ‘yan kasuwa, masana’antu, ma’adinai da noma ta Jihar Kaduna (KADCCIMA), Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, ya yi kira ga yankin Arewa da su tashi tsaye domin magance matsananciyar yunwa da za a iya fuskanta.

Da yake jawabi a wajen bikin karramawa na KADCCIMA karo na 3 da aka gudanar a Kaduna, Sarkin ya ce yankin ba ya bukatar boka da zai shaida musu cewa matsalar yunwa na tafe kuma ya kamata a farka domin noma shi ne ginshikin tattalin arziki.

  • An Ɗaure Mutum 14 Kan Yaɗa Bidiyon Maɗigo A Jamhuriyar Nijar
  • A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

A cewarsa, “Batun matsalar yunwa a shekara mai zuwa, ba ka bukatar boka ya gaya maka abin da zai faru, amma muna addu’a ga Ubangiji Madaukakin Sarki kuma wannan kira ne da ya kamata mutane su yi amfani da wasu hanyoyin da za su bi domin samun mafita, tabbas za ku fuskanci abubuwa wadanda ba a yi tsammani ba.

ADVERTISEMENT

“Ya kamata mu farka daga barcin da muke yi, mu yi abin da za mu iya yi domin ginshikin tattalin arzikinmu ni a ganina shi ne noma, musamman a yankin Arewa, noma ya samu mummunar illa a bana saboda wasu guda biyu, daya ambaliya, na biyu kuma ‘yan bindiga wanda duk abin takaici ne, a yankinmu wanda ke da hadari.”

Ya taya wadanda aka karrama murna, inda ya ce sun bayar da gudunmawa sosai ga tattalin arzikin kasar nan a fannonin rayuwa daban-daban musamman a yankin Arewa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Daga nan sai ya bayyana cewa makarantun gaba da sakandare a duniya ba kyauta ba ne inda ya ce, “Idan ‘yan Nijeriya suna son ilimi mai inganci, sai sun biya, ba wai ina cewa mutane su biye tsadar rayuwa ba saboda wasu kudaden rajistar da muke biya a makarantarmu ta Nijeriya idan har za a biya su, ka kwatanta shi da makarantun da ke ketare, za ka gano cewa muna biyan kudi kadan, idan aka kwatanta da Nijeriya”.

Shi ma da yake jawabi, Gwamna Nasir El-Rufai wanda ya samu wakilcin babban sakataren ma’aikatar kirkire-kirkire ta kasuwanci, Dakta Yusuf Saleh, ya ce a cikin shekaru bakwai da suka gabata gwamnatin Jihar Kaduna ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin ta zuba jari a sassa daban-daban na fannin tattalin arziki. .

Ya ce ma’aikatar kirkire-kirkire ta kasuwanci na bunkasa fasahar matasa don dacewa da al’amuran rayuwa daban-daban.

Shugaban masana’antun Falke, Alhaji Samaila Maigoro, ya bukaci gwamnati da ta zakulo sana’o’in da ake da su tare da karfafa musu gwiwa su kara himmatuwa ta hanyar kayayyakin aiki, horarwa da sauransu.

Shugaban KADCCIMA, Alhaji Sulieman Aliyu, ya ce kungiyar za ta bullo da wani shiri na ba da shawara ga shugabannin ‘yan kasuwa a yankin nan gaba.

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Goro

Goron Jumu'a

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.