• Leadership Hausa
Saturday, April 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

by Sadiq
5 months ago
in Labarai
0
Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai martaba Sarkin Zazzau kuma babban mataimaki na kungiyar ‘yan kasuwa, masana’antu, ma’adinai da noma ta Jihar Kaduna (KADCCIMA), Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, ya yi kira ga yankin Arewa da su tashi tsaye domin magance matsananciyar yunwa da za a iya fuskanta.

Da yake jawabi a wajen bikin karramawa na KADCCIMA karo na 3 da aka gudanar a Kaduna, Sarkin ya ce yankin ba ya bukatar boka da zai shaida musu cewa matsalar yunwa na tafe kuma ya kamata a farka domin noma shi ne ginshikin tattalin arziki.

  • An Ɗaure Mutum 14 Kan Yaɗa Bidiyon Maɗigo A Jamhuriyar Nijar
  • A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

A cewarsa, “Batun matsalar yunwa a shekara mai zuwa, ba ka bukatar boka ya gaya maka abin da zai faru, amma muna addu’a ga Ubangiji Madaukakin Sarki kuma wannan kira ne da ya kamata mutane su yi amfani da wasu hanyoyin da za su bi domin samun mafita, tabbas za ku fuskanci abubuwa wadanda ba a yi tsammani ba.

“Ya kamata mu farka daga barcin da muke yi, mu yi abin da za mu iya yi domin ginshikin tattalin arzikinmu ni a ganina shi ne noma, musamman a yankin Arewa, noma ya samu mummunar illa a bana saboda wasu guda biyu, daya ambaliya, na biyu kuma ‘yan bindiga wanda duk abin takaici ne, a yankinmu wanda ke da hadari.”

Ya taya wadanda aka karrama murna, inda ya ce sun bayar da gudunmawa sosai ga tattalin arzikin kasar nan a fannonin rayuwa daban-daban musamman a yankin Arewa.

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Daga nan sai ya bayyana cewa makarantun gaba da sakandare a duniya ba kyauta ba ne inda ya ce, “Idan ‘yan Nijeriya suna son ilimi mai inganci, sai sun biya, ba wai ina cewa mutane su biye tsadar rayuwa ba saboda wasu kudaden rajistar da muke biya a makarantarmu ta Nijeriya idan har za a biya su, ka kwatanta shi da makarantun da ke ketare, za ka gano cewa muna biyan kudi kadan, idan aka kwatanta da Nijeriya”.

Shi ma da yake jawabi, Gwamna Nasir El-Rufai wanda ya samu wakilcin babban sakataren ma’aikatar kirkire-kirkire ta kasuwanci, Dakta Yusuf Saleh, ya ce a cikin shekaru bakwai da suka gabata gwamnatin Jihar Kaduna ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin ta zuba jari a sassa daban-daban na fannin tattalin arziki. .

Ya ce ma’aikatar kirkire-kirkire ta kasuwanci na bunkasa fasahar matasa don dacewa da al’amuran rayuwa daban-daban.

Shugaban masana’antun Falke, Alhaji Samaila Maigoro, ya bukaci gwamnati da ta zakulo sana’o’in da ake da su tare da karfafa musu gwiwa su kara himmatuwa ta hanyar kayayyakin aiki, horarwa da sauransu.

Shugaban KADCCIMA, Alhaji Sulieman Aliyu, ya ce kungiyar za ta bullo da wani shiri na ba da shawara ga shugabannin ‘yan kasuwa a yankin nan gaba.

Tags: Ambaliyar RuwaKadunaNomaSarkin ZazzauTattalin ArzikiYunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Ɗaure Mutum 14 Kan Yaɗa Bidiyon Maɗigo A Jamhuriyar Nijar

Next Post

Goron Jumu’a

Related

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato
Labarai

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

9 hours ago
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 
Labarai

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

10 hours ago
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami
Labarai

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

11 hours ago
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso
Manyan Labarai

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

12 hours ago
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida
Manyan Labarai

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

12 hours ago
Elon Musk Ya Zarce Barack Obama Yawan Mabiya A Twitter
Manyan Labarai

Elon Musk Ya Zarce Barack Obama Yawan Mabiya A Twitter

14 hours ago
Next Post
Goro

Goron Jumu'a

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

March 31, 2023
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

March 31, 2023
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

March 31, 2023
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

March 31, 2023
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

March 31, 2023
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

March 31, 2023
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

March 31, 2023
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

March 31, 2023
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

March 31, 2023
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

March 31, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.