• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bude Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Wasa A Turai

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
An Bude Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Wasa A Turai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

An bude kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo a Ingila daga ranar Laraba 14 ga watan Yunin shekara ta 2023 zuwa 1 ga watan Satumbar 2023 kamar yadda aka saba yi duk shekara.

Kungiya za ta iya sayen dan wasan da bashi da yarjejeniya da wata kungiya, haka kuma za’a iya daukar aron dan wasa bisa kan doka da kulla kwantiragi bisa tsarin hukumar kwallon kafa ta duniya.

  • Mace Aba Ce Mai Daraja, Ba Sai Ta Ba Da Kanta Ba Za Ta Yi Suna A Fim – Jamila Saleh
  • Gwamnatin Neja Za Ta Fito Da Tsarin Ci gaban Jihar Na Shekaru 30

Haka kuma kungiya za ta iya daukar aron mai tsaron raga da zarar ba wani babban mai tsaron da yake da lafiya a kasa haka kuma za’a iya ciniki tsakanin kungiyoyin Premier League da ta EFL.

Kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a Ingila ta fara hada-hada daga ranar Laraba 14 ga watan Yunin 2023 zuwa 1 ga watan Satumbar 2023 kuma za’a iya kara wa’adi a karshen ranar rufe kasuwar idan an kusa kammala wani cinikin ko daukar aron dan wasa, amma lokaci bai ba da ikon cimma matsaya ba.

A Faransa kuma tun daga ranar 19 ga watan Yuni kasuwar ‘yan kwallo za ta fara ci a gasar Ligue 1 da sauran wasannin, wadda za ta karkare ranar 1 ga watan Satumbar 2023.

Sannan a kasashen Sipaniya da Jamus da Italiya kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a La Liga da Bundesliga da kuma Serie A za ta fara ci daga ranar 1 ga watan Yuli haka kuma za’a karkare hada-hada ranar 1 ga watan Satumbar 2023.

A kasar Amurka kuwa tuni aka ci kasuwar kwallon kafar Amurka daga 31 ga watan Janairun 2023 zuwa 24 ga watan Afirilun 2023 sannan za’a sake bude kasuwar daga 5 ga watan Yuli zuwa 2 ga watan Agustan 2023.

Ana fara kakar kwallon kafar Amurka daga 25 ga watan Fabrairu, wadda za ta rufe ranar 21 ga watan Oktoban 2023 wanda hakan yake nufin ba tare ake tafiya tsakanin Amurka da nahiyar turai ba.

Can kuwa a kasashen Argentina da Brazil tuni aka ci kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a Brazil, ana sa ran za’a sake yin hada-hada daga 14 ga watan Yuli zuwa 13 ga watan Agustan 2023.

An rufe kasuwar ranar 2 ga watan Fabrairun 2023, sai dai ba a bayyana ranar da za’a sake bude ta ba, amma ana sa ran sake cinikayya a cikin Yunin 2023 kamar yadda aka saba.

A Australia ma kasuwar cinikin ‘yan kwallo a Australia ta ci daga cikin Oktoba zuwa Mayu sannan za kuma a sake bude kasuwar daga 24 ga watan Yulin 2023 zuwa 15 ga watan Oktoban 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaCinikayyaTurai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hutun Haihuwa: An Samu Masu Yin Tazara 28,561 A Farkon 2023 A Jihar Gombe

Next Post

An Bukaci Musulman Nijeriya Su Fara Duban Watan Babbar Sallah Yau Lahadi

Related

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff
Wasanni

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

21 hours ago
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana
Wasanni

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

1 day ago
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa
Wasanni

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

2 days ago
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?
Wasanni

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

2 days ago
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

4 days ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

6 days ago
Next Post
Sarkin Musulmi Ya Sanar Da Ranar Asabar A Matsayin Ranar 1 Ga Muharram Na Shekarar 1444

An Bukaci Musulman Nijeriya Su Fara Duban Watan Babbar Sallah Yau Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.