ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bude Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Wasa A Turai

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Turai

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

ADVERTISEMENT

An bude kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo a Ingila daga ranar Laraba 14 ga watan Yunin shekara ta 2023 zuwa 1 ga watan Satumbar 2023 kamar yadda aka saba yi duk shekara.

Kungiya za ta iya sayen dan wasan da bashi da yarjejeniya da wata kungiya, haka kuma za’a iya daukar aron dan wasa bisa kan doka da kulla kwantiragi bisa tsarin hukumar kwallon kafa ta duniya.

  • Mace Aba Ce Mai Daraja, Ba Sai Ta Ba Da Kanta Ba Za Ta Yi Suna A Fim – Jamila Saleh
  • Gwamnatin Neja Za Ta Fito Da Tsarin Ci gaban Jihar Na Shekaru 30

Haka kuma kungiya za ta iya daukar aron mai tsaron raga da zarar ba wani babban mai tsaron da yake da lafiya a kasa haka kuma za’a iya ciniki tsakanin kungiyoyin Premier League da ta EFL.

Kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a Ingila ta fara hada-hada daga ranar Laraba 14 ga watan Yunin 2023 zuwa 1 ga watan Satumbar 2023 kuma za’a iya kara wa’adi a karshen ranar rufe kasuwar idan an kusa kammala wani cinikin ko daukar aron dan wasa, amma lokaci bai ba da ikon cimma matsaya ba.

A Faransa kuma tun daga ranar 19 ga watan Yuni kasuwar ‘yan kwallo za ta fara ci a gasar Ligue 1 da sauran wasannin, wadda za ta karkare ranar 1 ga watan Satumbar 2023.

Sannan a kasashen Sipaniya da Jamus da Italiya kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a La Liga da Bundesliga da kuma Serie A za ta fara ci daga ranar 1 ga watan Yuli haka kuma za’a karkare hada-hada ranar 1 ga watan Satumbar 2023.

A kasar Amurka kuwa tuni aka ci kasuwar kwallon kafar Amurka daga 31 ga watan Janairun 2023 zuwa 24 ga watan Afirilun 2023 sannan za’a sake bude kasuwar daga 5 ga watan Yuli zuwa 2 ga watan Agustan 2023.

Ana fara kakar kwallon kafar Amurka daga 25 ga watan Fabrairu, wadda za ta rufe ranar 21 ga watan Oktoban 2023 wanda hakan yake nufin ba tare ake tafiya tsakanin Amurka da nahiyar turai ba.

Can kuwa a kasashen Argentina da Brazil tuni aka ci kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a Brazil, ana sa ran za’a sake yin hada-hada daga 14 ga watan Yuli zuwa 13 ga watan Agustan 2023.

An rufe kasuwar ranar 2 ga watan Fabrairun 2023, sai dai ba a bayyana ranar da za’a sake bude ta ba, amma ana sa ran sake cinikayya a cikin Yunin 2023 kamar yadda aka saba.

A Australia ma kasuwar cinikin ‘yan kwallo a Australia ta ci daga cikin Oktoba zuwa Mayu sannan za kuma a sake bude kasuwar daga 24 ga watan Yulin 2023 zuwa 15 ga watan Oktoban 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25
Wasanni

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau
Wasanni

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
Next Post
Sarkin Musulmi Ya Sanar Da Ranar Asabar A Matsayin Ranar 1 Ga Muharram Na Shekarar 1444

An Bukaci Musulman Nijeriya Su Fara Duban Watan Babbar Sallah Yau Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.