• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Manoma Su Kara Yawan Kwakwar Manjan Da Suke Nomawa

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
An Bukaci Manoma Su Kara Yawan Kwakwar Manjan Da Suke Nomawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Sakataren Ma’aikatar Kasuwanci da Zuba Jari ta Tarayya, Nura Abba Rimi; ya bukaci masu ruwa da tsaki a fannin noman Kwakawar Manja, su yi amfani da fasahar zamani da kere-kere, don samar da girbi mai yawa tare da kokarin rage yin asara da kuma kara habaka fannin.

Rimi ya bayyana hakan ne, a wata ganawa da ya yi da masu ruwa da tsaki a fannin a garin Benin na Jihar Edo.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Jaddada Aniyar Karfafa Wa Mata Shiga Harkar Ma’adanai
  • Kotu Ta Hana ‘Yansanda Kama Shugabannin Jam’iyyar APC Da Suka Dakatar Da Ganduje A Kano

Har ila yau, ya kuma shawarce su da su rungumi amfani da dabarun kula da Bishiyoyin Kwakwar Manjan, musamman a gonakin da aka shuka su.

Wani jami’in a sashen kasuwanci na ma’aikatar, Gambo Garba Magaji; shi ne ya wakilici Babban Sakataren a wajen ganawar.
Kazalika, Rimi ya bukaci masu ruwa da tsakin; su yi duba a kan kalubalen da ke gabansu tare da yin aiki kafada da kafada, don tabbatar da ganin wannan fanni ya samu nasarar da ake bukata.

Jihohi shida ne suka halarci wannan ganawa, wadda sashen kasuwanci da fitar da kaya zuwa kasashen ketare na ma’aikatar ta kasuwanci da zuba jari ta tarayya ta shirya tare da hadaka da kungiyar masu samar da Kwakwar Manja ta kasa (NPPAN).

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Wadannan jihohi sun hada da Kuros Ribas, Akwa Ibom, Abiya, Imo, Edo da kuma Ondo.
Haka zalika, Rimi ya ce, “Dole ne mu yi duba a kan muhimmancin yin hadaka da ilimi, don habaka inganata hadakar ta hanyar yin amfani da hukumomin da ke gudanar da bincike da yin amfani da kwararrun da suke a masana’antu tare da yin amfani da hukumomin kasa da kasa”.

A cewarsa, ta hakan ne za mu samu irin kwarewar da suke da ita, musamman don kara habaka wannan noma na Kwakwar Manja a fadin wannan kasa baki-daya.

Shi ma a nasa jawabin, shugaban kungiyar Alphonsus Iyang, ya shawarci gwamnatin tarayya ta kirkiro da wuraren sarrafa Kwakwar Manja a daukacin jihohin da ke noma Kwakwar Manjan.

Ya ce, kirkiro da wadannan wurare ko shakka babu; zai taimaka wa kananan manoma da ke aiwatar da wannan noma na Kwakwar manja.

Shi kuwa Kwamishinan Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Abinci na Jihar, Stebe Ideheenre; kira ya yi da a mara wa masu ruwa da tsaki baya a wannan fanni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Manoman shinkafaNoman raniTsadar Abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Da Ya Sa Muka Tafi Amurka Don Taron Tsaro – Gwamna Radda

Next Post

Shugaba Xi Jinping Ya Wallafa Bayaninsa A Jaridar Faransa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

3 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

5 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

5 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

5 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Wallafa Bayaninsa A Jaridar Faransa

Shugaba Xi Jinping Ya Wallafa Bayaninsa A Jaridar Faransa

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.