ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Manoma Su Kara Yawan Kwakwar Manjan Da Suke Nomawa

by Abubakar Abba
2 years ago
Manoma

Babban Sakataren Ma’aikatar Kasuwanci da Zuba Jari ta Tarayya, Nura Abba Rimi; ya bukaci masu ruwa da tsaki a fannin noman Kwakawar Manja, su yi amfani da fasahar zamani da kere-kere, don samar da girbi mai yawa tare da kokarin rage yin asara da kuma kara habaka fannin.

Rimi ya bayyana hakan ne, a wata ganawa da ya yi da masu ruwa da tsaki a fannin a garin Benin na Jihar Edo.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Jaddada Aniyar Karfafa Wa Mata Shiga Harkar Ma’adanai
  • Kotu Ta Hana ‘Yansanda Kama Shugabannin Jam’iyyar APC Da Suka Dakatar Da Ganduje A Kano

Har ila yau, ya kuma shawarce su da su rungumi amfani da dabarun kula da Bishiyoyin Kwakwar Manjan, musamman a gonakin da aka shuka su.

ADVERTISEMENT

Wani jami’in a sashen kasuwanci na ma’aikatar, Gambo Garba Magaji; shi ne ya wakilici Babban Sakataren a wajen ganawar.
Kazalika, Rimi ya bukaci masu ruwa da tsakin; su yi duba a kan kalubalen da ke gabansu tare da yin aiki kafada da kafada, don tabbatar da ganin wannan fanni ya samu nasarar da ake bukata.

Jihohi shida ne suka halarci wannan ganawa, wadda sashen kasuwanci da fitar da kaya zuwa kasashen ketare na ma’aikatar ta kasuwanci da zuba jari ta tarayya ta shirya tare da hadaka da kungiyar masu samar da Kwakwar Manja ta kasa (NPPAN).

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

Wadannan jihohi sun hada da Kuros Ribas, Akwa Ibom, Abiya, Imo, Edo da kuma Ondo.
Haka zalika, Rimi ya ce, “Dole ne mu yi duba a kan muhimmancin yin hadaka da ilimi, don habaka inganata hadakar ta hanyar yin amfani da hukumomin da ke gudanar da bincike da yin amfani da kwararrun da suke a masana’antu tare da yin amfani da hukumomin kasa da kasa”.

A cewarsa, ta hakan ne za mu samu irin kwarewar da suke da ita, musamman don kara habaka wannan noma na Kwakwar Manja a fadin wannan kasa baki-daya.

Shi ma a nasa jawabin, shugaban kungiyar Alphonsus Iyang, ya shawarci gwamnatin tarayya ta kirkiro da wuraren sarrafa Kwakwar Manja a daukacin jihohin da ke noma Kwakwar Manjan.

Ya ce, kirkiro da wadannan wurare ko shakka babu; zai taimaka wa kananan manoma da ke aiwatar da wannan noma na Kwakwar manja.

Shi kuwa Kwamishinan Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Abinci na Jihar, Stebe Ideheenre; kira ya yi da a mara wa masu ruwa da tsaki baya a wannan fanni.

Manoma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Wallafa Bayaninsa A Jaridar Faransa

Shugaba Xi Jinping Ya Wallafa Bayaninsa A Jaridar Faransa

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.