ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Manoma Su Kara Yawan Kwakwar Manjan Da Suke Nomawa

by Abubakar Abba
2 years ago
Manoma

Babban Sakataren Ma’aikatar Kasuwanci da Zuba Jari ta Tarayya, Nura Abba Rimi; ya bukaci masu ruwa da tsaki a fannin noman Kwakawar Manja, su yi amfani da fasahar zamani da kere-kere, don samar da girbi mai yawa tare da kokarin rage yin asara da kuma kara habaka fannin.

Rimi ya bayyana hakan ne, a wata ganawa da ya yi da masu ruwa da tsaki a fannin a garin Benin na Jihar Edo.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Jaddada Aniyar Karfafa Wa Mata Shiga Harkar Ma’adanai
  • Kotu Ta Hana ‘Yansanda Kama Shugabannin Jam’iyyar APC Da Suka Dakatar Da Ganduje A Kano

Har ila yau, ya kuma shawarce su da su rungumi amfani da dabarun kula da Bishiyoyin Kwakwar Manjan, musamman a gonakin da aka shuka su.

ADVERTISEMENT

Wani jami’in a sashen kasuwanci na ma’aikatar, Gambo Garba Magaji; shi ne ya wakilici Babban Sakataren a wajen ganawar.
Kazalika, Rimi ya bukaci masu ruwa da tsakin; su yi duba a kan kalubalen da ke gabansu tare da yin aiki kafada da kafada, don tabbatar da ganin wannan fanni ya samu nasarar da ake bukata.

Jihohi shida ne suka halarci wannan ganawa, wadda sashen kasuwanci da fitar da kaya zuwa kasashen ketare na ma’aikatar ta kasuwanci da zuba jari ta tarayya ta shirya tare da hadaka da kungiyar masu samar da Kwakwar Manja ta kasa (NPPAN).

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

Wadannan jihohi sun hada da Kuros Ribas, Akwa Ibom, Abiya, Imo, Edo da kuma Ondo.
Haka zalika, Rimi ya ce, “Dole ne mu yi duba a kan muhimmancin yin hadaka da ilimi, don habaka inganata hadakar ta hanyar yin amfani da hukumomin da ke gudanar da bincike da yin amfani da kwararrun da suke a masana’antu tare da yin amfani da hukumomin kasa da kasa”.

A cewarsa, ta hakan ne za mu samu irin kwarewar da suke da ita, musamman don kara habaka wannan noma na Kwakwar Manja a fadin wannan kasa baki-daya.

Shi ma a nasa jawabin, shugaban kungiyar Alphonsus Iyang, ya shawarci gwamnatin tarayya ta kirkiro da wuraren sarrafa Kwakwar Manja a daukacin jihohin da ke noma Kwakwar Manjan.

Ya ce, kirkiro da wadannan wurare ko shakka babu; zai taimaka wa kananan manoma da ke aiwatar da wannan noma na Kwakwar manja.

Shi kuwa Kwamishinan Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Abinci na Jihar, Stebe Ideheenre; kira ya yi da a mara wa masu ruwa da tsaki baya a wannan fanni.

Manoma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Wallafa Bayaninsa A Jaridar Faransa

Shugaba Xi Jinping Ya Wallafa Bayaninsa A Jaridar Faransa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shari’ar Fiye Da Mutane 400 Da Ake Zargi Da Ta’addanci A Abuja

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shari’ar Fiye Da Mutane 400 Da Ake Zargi Da Ta’addanci A Abuja

June 15, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

June 15, 2026
Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

June 15, 2026
Beijing: An Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Game Da Gina JKS

Beijing: An Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Game Da Gina JKS

June 15, 2026
Ruben Amorim Na Dab Da Zama Sabon Kocin AC Milan

Ruben Amorim Na Dab Da Zama Sabon Kocin AC Milan

June 15, 2026
Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu

Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu

June 15, 2026
Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

June 15, 2026
Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.