ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Manoma Su Kara Yawan Kwakwar Manjan Da Suke Nomawa

by Abubakar Abba
2 years ago
Manoma

Babban Sakataren Ma’aikatar Kasuwanci da Zuba Jari ta Tarayya, Nura Abba Rimi; ya bukaci masu ruwa da tsaki a fannin noman Kwakawar Manja, su yi amfani da fasahar zamani da kere-kere, don samar da girbi mai yawa tare da kokarin rage yin asara da kuma kara habaka fannin.

Rimi ya bayyana hakan ne, a wata ganawa da ya yi da masu ruwa da tsaki a fannin a garin Benin na Jihar Edo.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Jaddada Aniyar Karfafa Wa Mata Shiga Harkar Ma’adanai
  • Kotu Ta Hana ‘Yansanda Kama Shugabannin Jam’iyyar APC Da Suka Dakatar Da Ganduje A Kano

Har ila yau, ya kuma shawarce su da su rungumi amfani da dabarun kula da Bishiyoyin Kwakwar Manjan, musamman a gonakin da aka shuka su.

ADVERTISEMENT

Wani jami’in a sashen kasuwanci na ma’aikatar, Gambo Garba Magaji; shi ne ya wakilici Babban Sakataren a wajen ganawar.
Kazalika, Rimi ya bukaci masu ruwa da tsakin; su yi duba a kan kalubalen da ke gabansu tare da yin aiki kafada da kafada, don tabbatar da ganin wannan fanni ya samu nasarar da ake bukata.

Jihohi shida ne suka halarci wannan ganawa, wadda sashen kasuwanci da fitar da kaya zuwa kasashen ketare na ma’aikatar ta kasuwanci da zuba jari ta tarayya ta shirya tare da hadaka da kungiyar masu samar da Kwakwar Manja ta kasa (NPPAN).

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Wadannan jihohi sun hada da Kuros Ribas, Akwa Ibom, Abiya, Imo, Edo da kuma Ondo.
Haka zalika, Rimi ya ce, “Dole ne mu yi duba a kan muhimmancin yin hadaka da ilimi, don habaka inganata hadakar ta hanyar yin amfani da hukumomin da ke gudanar da bincike da yin amfani da kwararrun da suke a masana’antu tare da yin amfani da hukumomin kasa da kasa”.

A cewarsa, ta hakan ne za mu samu irin kwarewar da suke da ita, musamman don kara habaka wannan noma na Kwakwar Manja a fadin wannan kasa baki-daya.

Shi ma a nasa jawabin, shugaban kungiyar Alphonsus Iyang, ya shawarci gwamnatin tarayya ta kirkiro da wuraren sarrafa Kwakwar Manja a daukacin jihohin da ke noma Kwakwar Manjan.

Ya ce, kirkiro da wadannan wurare ko shakka babu; zai taimaka wa kananan manoma da ke aiwatar da wannan noma na Kwakwar manja.

Shi kuwa Kwamishinan Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Abinci na Jihar, Stebe Ideheenre; kira ya yi da a mara wa masu ruwa da tsaki baya a wannan fanni.

Manoma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Wallafa Bayaninsa A Jaridar Faransa

Shugaba Xi Jinping Ya Wallafa Bayaninsa A Jaridar Faransa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Manoma

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Manoma

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.