• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Aiki Da Sashen Farko Na Layin Dogon Da Sin Ta Gina A Lagos 

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Fara Aiki Da Sashen Farko Na Layin Dogon Da Sin Ta Gina A Lagos 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya jagoranci kaddamar da sashen farko na layin dogon jiragen kasa masu amfani da lantarki, wanda kamfanin kasar Sin ya kammala ginawa a jihar Lagos dake kudancin kasar.

A jiya Talata ne shugaban na Najeriya tare da kusoshin gwamnati, da wakilai daga bangaren kasar Sin, suka kaddamar da layin dogon, wanda shi ne irin sa na farko a yammacin Afirka, da aka aiwatar karkashin shawarar ziri daya da hanya daya.

Tun a shekarar 2010 ne dai kamfanin gine gine na CCECC, ya fara aiwatar da ginin sashen farko na layin dogon mai tsayin kilomita 13 da tashoshi 5, cikin jimillar layin dogon da zai kai kilomita 27 idan an kammala shi baki daya. Kuma da zarar komai ya daidaita, za a rika jigilar fasinjoji sama da 250,000, cikin jiragen kasan da za su yi zirga zirga kan sashen na farko.

Yayin kaddamar da fara amfani da layin dogon, shugaba Buhari, ya jinjinawa karkon aikin, da nagarta, da kuma dadin tafiyar jirgin kasan.

Kaza lika a lokacin kaddamar da fara amfani da sashen na farko, an kuma aza tubalin ginin sashe na 2 mai tsayin kilomita 14.

Labarai Masu Nasaba

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya sheda bikin rattaba hannu kan wata sabuwar kwangilar gina sashe na biyu na layin dogo a cikin Legos domin saukaka harkokin sufuri a cikin birnin.

Da yake jawabin maraba, mataimakin gwamnan jihar Legos Femi Hamzat ya ce, “Wannan layin dogo da aka bude a wannan rana ta Talata zai taimaka wajen rage wahalhalu na sufuri da jama’a ke fuskanta a birnin Legos saboda yawan cunkoson ababen hawa, sannan kuma zai bunkasa tattalin arzikin jihar, kana zai saka jihar ta Legos cikin jerin manyan birane na duniya, kamar yadda kuka sani bukatar mutane dai ita ce a gabanmu. A don haka wannan aiki an yi shi ne domin al’ummar jihar Legos. Mai girma shugaban kasa ina so ka ba ni dama kuma domin mika godiya ga dukkannin wadanda suka taimaka wajen tabbatar da wannan aiki musamman ma kai kanka shugaban kasa da kamfanin kasar Sin.”

Shi kuwa da yake nasa jawabin, jakadan kasar Sin wato Mr. Cui Jianchun cewa ya yi, “Zan yi amfani da wannan dama wajen sanar da wasu mahimman batutuwa guda 3 na ci gaba da shugaba Xi ya kirkiro da su domin ci gaban duniya. Na farko muradun raya kasashen duniya, na biyu kuma tabbatar da tsaro a duniya baki daya, sai na uku kuma shirin zuba jari na biliyoyin daloli karkashin shirin tafiya kan gwadabe guda wajen tallafawa tattalin arzikin kasashe wanda ake yi wa lakabi da BRI Initiative, amma dai abin da Sin ta fi fifitawa shi ne kara samuwar hadin kai tsakaninta da kasashen Afrika. Mai girma shugaban kasa ina son na tabbatar maka cewa kudurce-kudurcen ci gaba guda 9 da shugaba Xi ya bujiro da su domin kasashen Afrika, Najeriya za ta amfana da manyan ayyuka har 15 daga kasar Sin. Ina da yakinin cewa muddin kasashen biyu za su yi aiki tare, tabbas kasar Sin za ta iya cimma burinta na kawata biranen Najeriya kamar yadda kasar Sin ta bunkasa a yanzu ta fuskar ababen more rayuwa. Ha’ila yau ina son na kara tabbatar wa Najeriya cewa nan da ’yan shekaru za mu iya cimma muradun nan guda 5 da kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ya tanadar wadanda suka kunshi hadin kai wajen bunkasar tattalin arziki, da hadin gwiwa wajen tabbatar da tsaro da diplomasiyya da yin aiki tare kana da bunkasa harkokin sadarwa tsakanin al`umma.”(Saminu Alhassan, Garba Abdullahi Bagwai)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gabatar Da Sakon Bidiyo Ga Taron Koli Karo Na 7 Na Kungiyar Kasashen Latin Amurka Da Caribbean

Next Post

Mutum 2 Sun Mutu, 9 Sun Bace Bayan Jirgin Ruwa Ya Nutse Tsakanin Japan Da Koriya Ta Kudu 

Related

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

20 hours ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

21 hours ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

22 hours ago
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
Daga Birnin Sin

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

23 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

2 days ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

2 days ago
Next Post
Mutum 2 Sun Mutu, 9 Sun Bace Bayan Jirgin Ruwa Ya Nutse Tsakanin Japan Da Koriya Ta Kudu 

Mutum 2 Sun Mutu, 9 Sun Bace Bayan Jirgin Ruwa Ya Nutse Tsakanin Japan Da Koriya Ta Kudu 

LABARAI MASU NASABA

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.