ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Aiki Da Sashen Farko Na Layin Dogon Da Sin Ta Gina A Lagos 

by CMG Hausa
3 years ago
Lagos

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya jagoranci kaddamar da sashen farko na layin dogon jiragen kasa masu amfani da lantarki, wanda kamfanin kasar Sin ya kammala ginawa a jihar Lagos dake kudancin kasar.

A jiya Talata ne shugaban na Najeriya tare da kusoshin gwamnati, da wakilai daga bangaren kasar Sin, suka kaddamar da layin dogon, wanda shi ne irin sa na farko a yammacin Afirka, da aka aiwatar karkashin shawarar ziri daya da hanya daya.

Tun a shekarar 2010 ne dai kamfanin gine gine na CCECC, ya fara aiwatar da ginin sashen farko na layin dogon mai tsayin kilomita 13 da tashoshi 5, cikin jimillar layin dogon da zai kai kilomita 27 idan an kammala shi baki daya. Kuma da zarar komai ya daidaita, za a rika jigilar fasinjoji sama da 250,000, cikin jiragen kasan da za su yi zirga zirga kan sashen na farko.

ADVERTISEMENT

Yayin kaddamar da fara amfani da layin dogon, shugaba Buhari, ya jinjinawa karkon aikin, da nagarta, da kuma dadin tafiyar jirgin kasan.

Kaza lika a lokacin kaddamar da fara amfani da sashen na farko, an kuma aza tubalin ginin sashe na 2 mai tsayin kilomita 14.

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya sheda bikin rattaba hannu kan wata sabuwar kwangilar gina sashe na biyu na layin dogo a cikin Legos domin saukaka harkokin sufuri a cikin birnin.

Da yake jawabin maraba, mataimakin gwamnan jihar Legos Femi Hamzat ya ce, “Wannan layin dogo da aka bude a wannan rana ta Talata zai taimaka wajen rage wahalhalu na sufuri da jama’a ke fuskanta a birnin Legos saboda yawan cunkoson ababen hawa, sannan kuma zai bunkasa tattalin arzikin jihar, kana zai saka jihar ta Legos cikin jerin manyan birane na duniya, kamar yadda kuka sani bukatar mutane dai ita ce a gabanmu. A don haka wannan aiki an yi shi ne domin al’ummar jihar Legos. Mai girma shugaban kasa ina so ka ba ni dama kuma domin mika godiya ga dukkannin wadanda suka taimaka wajen tabbatar da wannan aiki musamman ma kai kanka shugaban kasa da kamfanin kasar Sin.”

Shi kuwa da yake nasa jawabin, jakadan kasar Sin wato Mr. Cui Jianchun cewa ya yi, “Zan yi amfani da wannan dama wajen sanar da wasu mahimman batutuwa guda 3 na ci gaba da shugaba Xi ya kirkiro da su domin ci gaban duniya. Na farko muradun raya kasashen duniya, na biyu kuma tabbatar da tsaro a duniya baki daya, sai na uku kuma shirin zuba jari na biliyoyin daloli karkashin shirin tafiya kan gwadabe guda wajen tallafawa tattalin arzikin kasashe wanda ake yi wa lakabi da BRI Initiative, amma dai abin da Sin ta fi fifitawa shi ne kara samuwar hadin kai tsakaninta da kasashen Afrika. Mai girma shugaban kasa ina son na tabbatar maka cewa kudurce-kudurcen ci gaba guda 9 da shugaba Xi ya bujiro da su domin kasashen Afrika, Najeriya za ta amfana da manyan ayyuka har 15 daga kasar Sin. Ina da yakinin cewa muddin kasashen biyu za su yi aiki tare, tabbas kasar Sin za ta iya cimma burinta na kawata biranen Najeriya kamar yadda kasar Sin ta bunkasa a yanzu ta fuskar ababen more rayuwa. Ha’ila yau ina son na kara tabbatar wa Najeriya cewa nan da ’yan shekaru za mu iya cimma muradun nan guda 5 da kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ya tanadar wadanda suka kunshi hadin kai wajen bunkasar tattalin arziki, da hadin gwiwa wajen tabbatar da tsaro da diplomasiyya da yin aiki tare kana da bunkasa harkokin sadarwa tsakanin al`umma.”(Saminu Alhassan, Garba Abdullahi Bagwai)

 

Lagos
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Next Post
Mutum 2 Sun Mutu, 9 Sun Bace Bayan Jirgin Ruwa Ya Nutse Tsakanin Japan Da Koriya Ta Kudu 

Mutum 2 Sun Mutu, 9 Sun Bace Bayan Jirgin Ruwa Ya Nutse Tsakanin Japan Da Koriya Ta Kudu 

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.