• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gama Kashi Na Farko Na Ginin Yankin Raya Masana’antu Na PK24 A Cote d’Ivoire Bisa Taimakon Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Gama Kashi Na Farko Na Ginin Yankin Raya Masana’antu Na PK24 A Cote d’Ivoire Bisa Taimakon Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 23 ga wata, aka kammala kashi na farko na aikin ginin yankin raya masana’antu na PK24 da kamfanin gina tashoshin jiragen ruwa na kasar Sin na CHEC ya gudanar a kasar Cote d’Ivoire.

A jawabin da ya gabatar yayin bikin kammala aikin, firaministan kasar Cote d’Ivoire Patrick Achi Jérôme ya bayyana cewa, wannan babban aikin zai taimaka wajen kyautata hanyar raya tattalin arzikin kasar, da farfado da masana’antun kasar. Ya kuma karfafawa kamfanoni gwiwa, da su zauna da gindinsu a yankin raya masana’antu na PK24, a kokarin bayar da gudummawa ga ci gaban tattalin arziki da samar da guraben ayyukan yi ga matasan kasar.

  • Wang Yi Ya Yaba Da Ayyukan Diflomasiyyar Kasar Sin A Shekarar 2022

A nasa bangaren kuma, Souleymane Diarrassouba, ministan cinikyayya da masana’antun kasar Cote d’Ivoire ya ce, kamfanin CHEC ya haye dimbin wahalhalu yayin gudanar da aikin, kafin ya gama aikin gina wannan yankin raya masana’antu na zamani da ke da karfin takara sosai.

Haka kuma, yayin da babban manajan yankin yammacin Afirka na kamfanin CHEC Wang Guangsheng ke zantawa da wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin, ya bayyana cewa, bayan kammala aikin, za a jawo karin kamfanoni da su zuba jari, ta yadda za a samar da dimbin guraben ayyukan yi ga mazauna wurin.

Kashi na farko na yankin raya masana’atu na PK24, yana arewa maso yammacin birnin Abidjan, babban birnin kasar Cote d’Ivoire, wanda fadinsa ya kai kadada 127, kuma an fara aikin gina shi a ranar 1 ga watan Fabrairu na shekarar 2020.(Kande Gao)

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Tsira Daga Lokaci Mafi Wahala

Next Post

Shugaban Kasar Sin Ya Taya Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Kamfanin Wasannin Fasaha Na Oriental Na Kasar Sin

Related

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

7 minutes ago
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

16 hours ago
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala
Daga Birnin Sin

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

18 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

20 hours ago
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

21 hours ago
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

23 hours ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Taya Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Kamfanin Wasannin Fasaha Na Oriental Na Kasar Sin

Shugaban Kasar Sin Ya Taya Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Kamfanin Wasannin Fasaha Na Oriental Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.