ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gama Kashi Na Farko Na Ginin Yankin Raya Masana’antu Na PK24 A Cote d’Ivoire Bisa Taimakon Kasar Sin

by CMG Hausa
4 years ago
Cote d’Ivoire

Ranar 23 ga wata, aka kammala kashi na farko na aikin ginin yankin raya masana’antu na PK24 da kamfanin gina tashoshin jiragen ruwa na kasar Sin na CHEC ya gudanar a kasar Cote d’Ivoire.

A jawabin da ya gabatar yayin bikin kammala aikin, firaministan kasar Cote d’Ivoire Patrick Achi Jérôme ya bayyana cewa, wannan babban aikin zai taimaka wajen kyautata hanyar raya tattalin arzikin kasar, da farfado da masana’antun kasar. Ya kuma karfafawa kamfanoni gwiwa, da su zauna da gindinsu a yankin raya masana’antu na PK24, a kokarin bayar da gudummawa ga ci gaban tattalin arziki da samar da guraben ayyukan yi ga matasan kasar.

  • Wang Yi Ya Yaba Da Ayyukan Diflomasiyyar Kasar Sin A Shekarar 2022

A nasa bangaren kuma, Souleymane Diarrassouba, ministan cinikyayya da masana’antun kasar Cote d’Ivoire ya ce, kamfanin CHEC ya haye dimbin wahalhalu yayin gudanar da aikin, kafin ya gama aikin gina wannan yankin raya masana’antu na zamani da ke da karfin takara sosai.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, yayin da babban manajan yankin yammacin Afirka na kamfanin CHEC Wang Guangsheng ke zantawa da wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin, ya bayyana cewa, bayan kammala aikin, za a jawo karin kamfanoni da su zuba jari, ta yadda za a samar da dimbin guraben ayyukan yi ga mazauna wurin.

Kashi na farko na yankin raya masana’atu na PK24, yana arewa maso yammacin birnin Abidjan, babban birnin kasar Cote d’Ivoire, wanda fadinsa ya kai kadada 127, kuma an fara aikin gina shi a ranar 1 ga watan Fabrairu na shekarar 2020.(Kande Gao)

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

 

Cote d’Ivoire
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026
Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

July 23, 2026
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Taya Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Kamfanin Wasannin Fasaha Na Oriental Na Kasar Sin

Shugaban Kasar Sin Ya Taya Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Kamfanin Wasannin Fasaha Na Oriental Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Cote d’Ivoire

Wasiƙar Trump Ba Za Ta Ceto Tinubu Daga Faduwa Zaɓe Ba – Jam’iyyar ADC

July 24, 2026
Falalar Yawaita Istigifari (2)

Falalar Yawaita Istigifari (2)

July 24, 2026
Cote d’Ivoire

Amurka Ta Kakaba Harajin Kaso 12.5% A Kan kayayyakin Nijeriya

July 24, 2026
Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

July 24, 2026
Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

July 24, 2026
NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

July 24, 2026
Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.