• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Al'ajabi
0
An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekara 2015, Sulemana Abdul Samed ya farka daga barci, amma sai wani abu ya bashi mamaki domin ya lura cewa harshensa ya kara girma har ya cika masa baki ta yadda baya iya yin numfashi sosai.

Bayan ya sha magani da ya sayo a wani kemis, wanda ya rage kumburin harshen, dan makarantar babbar sakandaren bai san cewa wannan lamarin zai sauya rayuwarsa gaba daya ba.

  • Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha – Shugaban NBA
  • An Nemi Fulani Su Manta Da Bambancin Da Ke Tsakaninsu Don Kubuta Daga Matsalar Tsaro

Kuma daga wancan lokacin zuwa yanzu, Sulemana wanda aka fi sani da sunan Awuche- ya rika kara tsawo har sai da ya kai kafa 9.6 kuma ya ci gaba da kara tsawo.

“Cikin kowane wata uku zuwa wata hudu na ke kara tsawo. Idan ba ka gan ni cikin wata uku ko hudu ba, za ka na kara tsawo,” in ji Awuche yayin da yake hira da wakilin BBC Pidgin Fabour Nunoo.

Tsawon da Awuche ya yi ya sa ya zama wani shahararre a garinsu Gambaga yayin da mazauna garin daga kananansu har zuwa dattawan garin ke kallonsa da ta’ajibi.

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

“Akwai lokacin da wani dan sanda ya ce nazarce shi da tsawona, saboda haka ya ce zai dauki hoto tare da ni,” kamar yadda ya tuna.

Daga ‘yan siyasa zuwa ga jami’an soji da na ‘yansanda duka suna farin ciki da zarar sunga Awuche, wanda baya ga cewa ya fi kowa tsawo, yana kuma da kyawun mu’amala da sauran jama’a.

“Tsawona ya mayar da ni sahahrarre,”kamar yadda ya shaida wa wakilin BBC wanda ya ziyarci garin na Awuche.

Ya kuma ce da a duk lokacin da ya halarci wani biki, sai mutane a wurin su rika matsowa kusa da shi kuma yana son haka sosai.

Ya kan kuma ba su damar daukar hoto da shi a duk lokacin da suka bukaci haka.

“Likitoci sun ce tsawona na lalura ce mai suna ‘gigantism’ Tsawon da Awuche ya yi ba irin wanda aka saba gani ba ne, domin ko likitoci na kiransa da sunan ‘gigantism’ da turancin Ingilishi.

Sun ce wannan matsala ce da kan sa mutum ya yi tsawon da ya zarce na yawancin mutane.

“Yayin da na je asibitin BMC, sai wani mutum farar fata ya ganni kuma sai ya ce ina da lalurar gigantism.

“Ya kuma ce wani likitan da ya rika duba lafiyarsa ya shaida masa cewa akwai wani abu a cikin kwakwalwarsa da ya kamata a yi masa tiyata domin a cire shi.

Ya ce wannan abin ne ke sa kashinsa ke kara girma da tsawo sosai, kuma ya ce idan ba a cire wannan abin daga kwakwalwarsa ba, ba zai daina tsawo ba kuma wannan kai ya shafar lafiyarsa da ingancin walwala da jin dadin rayuwarsa.

Amma duk da haka Awuche yana fatan yin aure da haihuwar ‘ya’ya, wadanda ya ce yake son ganin yadda za su kasance.

Kuma bai damu da cewa ya fi kowa tsawo ba, domin ya ce haka Allah ya so ya gan shi kenan.

Mun ciro muku daga BBC.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BBCCutaDalibiMamakiMutaneTsawo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha – Shugaban NBA

Next Post

Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

Related

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

1 week ago
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

3 weeks ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

3 weeks ago
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

3 months ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

4 months ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

4 months ago
Next Post
Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.