• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Jami’an EFCC 2 Kan Zargin Kisan Abokin AikinsuĀ 

by CMG Hausa
2 years ago
in Labarai
0
An Gurfanar Da Jami’an EFCC 2 Kan Zargin Kisan Abokin AikinsuĀ 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Yaki da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC) ta ce, wani jami’inta mai suna Insifekta Abel Isah Dickson ya mutu bayan rashin jituwa da hatsaniya da ta shiga tsakaninsu da wasu abokan aikinsa guda biyu kan wasu kayayyakin da aka amso daga wajen wani da ake zargi a Jihar Sokoto.Ā 

 

Kakakin hukumar ta EFCC, Wilson Uwujaren, ya ce, kayayyakin sun hada da magunguna da wasu kudade.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Lasisin Bude Jami’ar Koyo Daga Gida Da Karin Wasu 37

EFCC ta bayyana sunayen jami’an biyu sun hada da Mataimakin Sufuritendan hukumar EFCC, Apata Oluwaseun Odunayo da Insifekta na hukumar EFCC, Ogbuji Titu Tochukwu, wadanda tunin aka cafke su tare da gurfanar da su a kotu a jihar Sokoto kan zargin kisan kai.

 

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

Uwujaren ya kuma ce, shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa, za su tabbatar an wanzar da adalci wajen hukunta jami’an, ya ce, an dakatar da jami’an biyu yayin da bincike ke cigaba da gudana.

 

Ya ce, Bawa ya sha alwashin ba zai lamunci wani dabi’a ta rashin da’a ba, “Shugabanmu, Abdulrasheed Bawa, ya kadu da wannan lamarin kuma ya jajantawa iyalan jami’in da ya rasa ransa.

 

ā€œYa kuma tabbatar da cewa jami’an da suka yi sanadiyyar rasa jami’in namu tabbas za su fuskanci hukunci har sai adalci ya wanzu.”

 

Kazalika, Bawa ya gargadi jami’ansa da su daina kokarin kauce wa ka’idar aiki da koyarwar da aka musu. Ya nuna cewa ba za su lamunci rashin bin matakan aiki da koyarwar da aka yi wa jami’an ba.

 

“A halin da ake ciki, an bisne jami’in namu da ya mutu a ranar Asabar 13 ga watan Mayun 2023 a Jos ta jihar Filato.”

 

“Matashin jami’in namu ya mutu ne a ranar 7 ga watan Mayun 2023 a asibitin koyarwa na jami’ar Usmanu DanFodiyo da ke Sokoto yayin da ke amsar kulawar Likitoci bayan raunukan da ya samu kwanaki biyu kafin nan a wani hatsaniyar da ya barke tsakaninsa da wasu jami’anmu biyu masu suna Apata Oluwaseun Odunayo da Insifekta Ogbuji Titu Tochukwu.

 

“Sun samu rashin jituwar ne kan wasu tsarin ajiye wasu kaya mallakin wani da ake zargi da ke tsare, hakan ya kai su ga yin fada, lamarin da hukumar nan ta yi tir da shi.

 

“Jami’an biyu an dakatar da su kuma an mikasu ga ‘yansandan Nijeriya inda suka gurfanar da su.

 

“An shigar da su kara ne kan zarge-zargen guda biyu da suka hada da hada baki wajen aikata kisan gilla a gaban babban Kotun Majistire, Gwiwa da ke Sokoto.”

 

ā€œLaifukan biyun su na da hukunci a karkashin sashe na 60 da na 191 na dokar final kod ta Jihar Sokoto, 2019.

 

“Ba tare da nuna kyama ga binciken ‘yan sanda ba, za su kuma fuskanci karin matakan ladabtarwa bisa ka’idojin ma’aikatan hukumar.”


Daga kanmu, magana ta ʙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Magana Maras Dacewa Ta Jakada Brigety Na Tare Da Wani Makasudi

Next Post

Darajar Hajojin Da Masana’antun Sin Ke Sarrafawa Ta Karu Zuwa Kaso 5.6 Bisa Dari A Afirilu

Related

Labarai

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

6 minutes ago
EFCC
Labarai

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

1 hour ago
ʘungiyar Sadarwa Ta ʘasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu
Labarai

ʘungiyar Sadarwa Ta ʘasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

1 hour ago
Mambobin APC Sun Buʙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle
Labarai

Mambobin APC Sun Buʙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

4 hours ago
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Manyan Labarai

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

5 hours ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

19 hours ago
Next Post
Darajar Hajojin Da Masana’antun Sin Ke Sarrafawa Ta Karu Zuwa Kaso 5.6 Bisa Dari A Afirilu

Darajar Hajojin Da Masana’antun Sin Ke Sarrafawa Ta Karu Zuwa Kaso 5.6 Bisa Dari A Afirilu

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

May 10, 2025
EFCC

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

May 10, 2025
ʘungiyar Sadarwa Ta ʘasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

ʘungiyar Sadarwa Ta ʘasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

May 10, 2025
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

May 10, 2025
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buʙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buʙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

May 10, 2025
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Talla

Ā© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

Ā© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.