• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Hallaka Matashi 1, An Jikkata Wani A Yakin Zaben APC A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Hallaka Matashi 1, An Jikkata Wani A Yakin Zaben APC A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutum daya ne aka tabbatar mutuwarsa yayin da wani guda kuma ya samu rauni sakamakon harbin bindiga da ake zargin daya daga cikin jami’an tsaro a tawagar dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi, Air Marshal Sadique Baba Abubakar (Mai ritaya) ya yi a kauyen Akuyam da ke karamar hukumar Dambam a Jihar Bauchi.

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, kakakin ‘yansandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, ga ‘yan jarida ya shaida cewar, “Abin da ya faru shi ne a ranar Litinin da karfe 8:30 na dare, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC, Air Marshal Sadique Baba Abubakar a lokacin da yake hanyarsa daga Dambam zuwa Akuyam domin yakin neman zabe, gab da shigarsu cikin Akuyam an kai farmaki ga tawagarsa.”

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano
  • Marwa Ya Sadaukar Da Karramawar LEADERSHIP Ga Buhari Da Jami’an NDLEA

Kamar yadda yake cewa, bayan harin da aka kai wa tawagar dan takarar APC din, daya daga cikin masu tsaro a tawagar ya bude wuta inda ya samu mutum biyu masu suna Saleh Garba (Dan shekara 35) da kuma Yakubu Yunusa (Dan shekara 20) dukkaninsu mazauna kauyen Akuyam kuma an kaisu zuwa asibitin FMC da ke Azare domin kulawar Likitoci.

Ya kara da cewa, “A ranar Talata muka samu tabbacin cewa daya daga cikinsu ya mutu a lokacin da yake amsar kulawar Likitoci. Tunin kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, Aminu Alhassan ya bada umarnin a kaddamar da bincike kan lamarin. Ya yi addu’ar Allah ya jikan wanda ya rasu.”

Kakakin ‘yan sandan ya kara da cewa, a ranar 24 ga watan Nuwamba kwamishinan ‘yansanda ya gana da jam’iyyun siyasa inda ya nemi jam’iyyun da su gudanar da harkokin siyasarsu bisa kan ka’ida tare bin dokokin zabe gami da nemansu da su yi siyasa ba da gaba ba.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

A bangarensu kwamitin yakin zaben dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi na jam’iyyar APC, Air Marshal Sadique Baba Abubakar, ya shaida cewar, ba su kai hari ga kowa ba illa ma su ne ‘yan adawarsu suka farmaka a kauyen Akuyam da ke karamar hukumar Dambam ya yin da suke cigaba da yakin zaben.

Da ya ke zantawa da manema labarai, daraktan yada labarai na kwamitin yakin zaben, Alhaji Salisu Barau, ya ce, duk da harin da aka kaddamar a kansu amma sun hana magoya bayansu maida martani domin kare rayuka da dukiya.

Barau ya kara da cewa an lalata musu motoci a kalla 15 zuwa 20 gami da jikkata wasu daga cikin mutanensu.

“Wasu mutane sun hau kan Bishiyoyi suna jifa da duwatsu dukka a kanmu. Mun samu mun tsira.”

Da aka tambayeshi ko su waye suka dauki nauyin harin, Barau ya shaida cewar, “Yan adawa ne suka dauka nauyin harin.” Da aka tambayeshi ko zai fayyace wasu ‘yan adawa ya sake nanata cewa dai ‘yan adawarsu ne.

“A fayyace yake ‘yan adawarmu ne suka kawo mana harin, saboda ba sai yiyu mu farmaki kanmu da kanmu ba.”

Ya cigaba da cewa, “Mun je Misa babu abun da ya faru illa ma dandazon jama’a da suka nuna mana kauna, Muna je Daraso, muka tsaya a Sade zuwa Hardawa dukka babu Wanda ya kai mana farmaki kuma ba mu farmaki kowa ba. Meye sa sai a Akuyam?.”

Da yake magana kan harin kuwa, Barau ya ce tun ma daren ranar Lahadi aka fara Kai musu harin a lokacin da suka yi kokarin shiga yankin Akuyam domin yakin zabe.

Ya tabbatar da cewa dan takararsu na gwamna mutum ne Mai son zaman lafiya da kwanciyar hankali don haka ba zai so kai ma wani ko wasu hari ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBauchiKamfe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kashi 50 Na Magungunan Afrika Jabu Ne – Majalisar Dinkin Duniya

Next Post

PDP Na Son A Yi Bincike Kan Kisan Matashi A Yakin Zaben APC A Bauchi 

Related

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000
Manyan Labarai

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

2 hours ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 hours ago
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano
Manyan Labarai

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

5 hours ago
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi
Manyan Labarai

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

9 hours ago
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil
Manyan Labarai

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

10 hours ago
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano
Manyan Labarai

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

20 hours ago
Next Post
PDP Na Son A Yi Bincike Kan Kisan Matashi A Yakin Zaben APC A Bauchi 

PDP Na Son A Yi Bincike Kan Kisan Matashi A Yakin Zaben APC A Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

August 28, 2025
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

August 28, 2025
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

August 28, 2025
Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

August 28, 2025
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

August 28, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

August 28, 2025
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

August 28, 2025
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

August 28, 2025
Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.