ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Hallaka Matashi 1, An Jikkata Wani A Yakin Zaben APC A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Akalla mutum daya ne aka tabbatar mutuwarsa yayin da wani guda kuma ya samu rauni sakamakon harbin bindiga da ake zargin daya daga cikin jami’an tsaro a tawagar dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi, Air Marshal Sadique Baba Abubakar (Mai ritaya) ya yi a kauyen Akuyam da ke karamar hukumar Dambam a Jihar Bauchi.

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, kakakin ‘yansandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, ga ‘yan jarida ya shaida cewar, “Abin da ya faru shi ne a ranar Litinin da karfe 8:30 na dare, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC, Air Marshal Sadique Baba Abubakar a lokacin da yake hanyarsa daga Dambam zuwa Akuyam domin yakin neman zabe, gab da shigarsu cikin Akuyam an kai farmaki ga tawagarsa.”

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano
  • Marwa Ya Sadaukar Da Karramawar LEADERSHIP Ga Buhari Da Jami’an NDLEA

Kamar yadda yake cewa, bayan harin da aka kai wa tawagar dan takarar APC din, daya daga cikin masu tsaro a tawagar ya bude wuta inda ya samu mutum biyu masu suna Saleh Garba (Dan shekara 35) da kuma Yakubu Yunusa (Dan shekara 20) dukkaninsu mazauna kauyen Akuyam kuma an kaisu zuwa asibitin FMC da ke Azare domin kulawar Likitoci.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “A ranar Talata muka samu tabbacin cewa daya daga cikinsu ya mutu a lokacin da yake amsar kulawar Likitoci. Tunin kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, Aminu Alhassan ya bada umarnin a kaddamar da bincike kan lamarin. Ya yi addu’ar Allah ya jikan wanda ya rasu.”

Kakakin ‘yan sandan ya kara da cewa, a ranar 24 ga watan Nuwamba kwamishinan ‘yansanda ya gana da jam’iyyun siyasa inda ya nemi jam’iyyun da su gudanar da harkokin siyasarsu bisa kan ka’ida tare bin dokokin zabe gami da nemansu da su yi siyasa ba da gaba ba.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A bangarensu kwamitin yakin zaben dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi na jam’iyyar APC, Air Marshal Sadique Baba Abubakar, ya shaida cewar, ba su kai hari ga kowa ba illa ma su ne ‘yan adawarsu suka farmaka a kauyen Akuyam da ke karamar hukumar Dambam ya yin da suke cigaba da yakin zaben.

Da ya ke zantawa da manema labarai, daraktan yada labarai na kwamitin yakin zaben, Alhaji Salisu Barau, ya ce, duk da harin da aka kaddamar a kansu amma sun hana magoya bayansu maida martani domin kare rayuka da dukiya.

Barau ya kara da cewa an lalata musu motoci a kalla 15 zuwa 20 gami da jikkata wasu daga cikin mutanensu.

“Wasu mutane sun hau kan Bishiyoyi suna jifa da duwatsu dukka a kanmu. Mun samu mun tsira.”

Da aka tambayeshi ko su waye suka dauki nauyin harin, Barau ya shaida cewar, “Yan adawa ne suka dauka nauyin harin.” Da aka tambayeshi ko zai fayyace wasu ‘yan adawa ya sake nanata cewa dai ‘yan adawarsu ne.

“A fayyace yake ‘yan adawarmu ne suka kawo mana harin, saboda ba sai yiyu mu farmaki kanmu da kanmu ba.”

Ya cigaba da cewa, “Mun je Misa babu abun da ya faru illa ma dandazon jama’a da suka nuna mana kauna, Muna je Daraso, muka tsaya a Sade zuwa Hardawa dukka babu Wanda ya kai mana farmaki kuma ba mu farmaki kowa ba. Meye sa sai a Akuyam?.”

Da yake magana kan harin kuwa, Barau ya ce tun ma daren ranar Lahadi aka fara Kai musu harin a lokacin da suka yi kokarin shiga yankin Akuyam domin yakin zabe.

Ya tabbatar da cewa dan takararsu na gwamna mutum ne Mai son zaman lafiya da kwanciyar hankali don haka ba zai so kai ma wani ko wasu hari ba.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
PDP Na Son A Yi Bincike Kan Kisan Matashi A Yakin Zaben APC A Bauchi 

PDP Na Son A Yi Bincike Kan Kisan Matashi A Yakin Zaben APC A Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.