ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Hallaka Matashi 1, An Jikkata Wani A Yakin Zaben APC A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Akalla mutum daya ne aka tabbatar mutuwarsa yayin da wani guda kuma ya samu rauni sakamakon harbin bindiga da ake zargin daya daga cikin jami’an tsaro a tawagar dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi, Air Marshal Sadique Baba Abubakar (Mai ritaya) ya yi a kauyen Akuyam da ke karamar hukumar Dambam a Jihar Bauchi.

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, kakakin ‘yansandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, ga ‘yan jarida ya shaida cewar, “Abin da ya faru shi ne a ranar Litinin da karfe 8:30 na dare, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC, Air Marshal Sadique Baba Abubakar a lokacin da yake hanyarsa daga Dambam zuwa Akuyam domin yakin neman zabe, gab da shigarsu cikin Akuyam an kai farmaki ga tawagarsa.”

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano
  • Marwa Ya Sadaukar Da Karramawar LEADERSHIP Ga Buhari Da Jami’an NDLEA

Kamar yadda yake cewa, bayan harin da aka kai wa tawagar dan takarar APC din, daya daga cikin masu tsaro a tawagar ya bude wuta inda ya samu mutum biyu masu suna Saleh Garba (Dan shekara 35) da kuma Yakubu Yunusa (Dan shekara 20) dukkaninsu mazauna kauyen Akuyam kuma an kaisu zuwa asibitin FMC da ke Azare domin kulawar Likitoci.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “A ranar Talata muka samu tabbacin cewa daya daga cikinsu ya mutu a lokacin da yake amsar kulawar Likitoci. Tunin kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, Aminu Alhassan ya bada umarnin a kaddamar da bincike kan lamarin. Ya yi addu’ar Allah ya jikan wanda ya rasu.”

Kakakin ‘yan sandan ya kara da cewa, a ranar 24 ga watan Nuwamba kwamishinan ‘yansanda ya gana da jam’iyyun siyasa inda ya nemi jam’iyyun da su gudanar da harkokin siyasarsu bisa kan ka’ida tare bin dokokin zabe gami da nemansu da su yi siyasa ba da gaba ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

A bangarensu kwamitin yakin zaben dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi na jam’iyyar APC, Air Marshal Sadique Baba Abubakar, ya shaida cewar, ba su kai hari ga kowa ba illa ma su ne ‘yan adawarsu suka farmaka a kauyen Akuyam da ke karamar hukumar Dambam ya yin da suke cigaba da yakin zaben.

Da ya ke zantawa da manema labarai, daraktan yada labarai na kwamitin yakin zaben, Alhaji Salisu Barau, ya ce, duk da harin da aka kaddamar a kansu amma sun hana magoya bayansu maida martani domin kare rayuka da dukiya.

Barau ya kara da cewa an lalata musu motoci a kalla 15 zuwa 20 gami da jikkata wasu daga cikin mutanensu.

“Wasu mutane sun hau kan Bishiyoyi suna jifa da duwatsu dukka a kanmu. Mun samu mun tsira.”

Da aka tambayeshi ko su waye suka dauki nauyin harin, Barau ya shaida cewar, “Yan adawa ne suka dauka nauyin harin.” Da aka tambayeshi ko zai fayyace wasu ‘yan adawa ya sake nanata cewa dai ‘yan adawarsu ne.

“A fayyace yake ‘yan adawarmu ne suka kawo mana harin, saboda ba sai yiyu mu farmaki kanmu da kanmu ba.”

Ya cigaba da cewa, “Mun je Misa babu abun da ya faru illa ma dandazon jama’a da suka nuna mana kauna, Muna je Daraso, muka tsaya a Sade zuwa Hardawa dukka babu Wanda ya kai mana farmaki kuma ba mu farmaki kowa ba. Meye sa sai a Akuyam?.”

Da yake magana kan harin kuwa, Barau ya ce tun ma daren ranar Lahadi aka fara Kai musu harin a lokacin da suka yi kokarin shiga yankin Akuyam domin yakin zabe.

Ya tabbatar da cewa dan takararsu na gwamna mutum ne Mai son zaman lafiya da kwanciyar hankali don haka ba zai so kai ma wani ko wasu hari ba.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
PDP Na Son A Yi Bincike Kan Kisan Matashi A Yakin Zaben APC A Bauchi 

PDP Na Son A Yi Bincike Kan Kisan Matashi A Yakin Zaben APC A Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.