Babban bankin kasuwancin kasar Rwanda dake bayar da rance, wato Bank of Kigali da Ant Group, daya daga manyan masu samar da hidimar fasaha ga kasuwancin kasar Sin, sun kaddamar da hidimar biyan kudi daga Rwanda zuwa kasar Sin ranar Alhamis din da ta gabata a Kigali, babban birnin kasar.
Ana sa ran hidimar wadda ke karkashin harkokin kudi kamar yadda yake kunshi cikin tsarin cinikayya ta zamani na kasa da kasa, za ta bunkasa harkokin kasuwanci tsakanin kasashen biyu. (Mai fassarawa: Ibrahim daga CMG Hausa)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp