An kaddamar da wani yankin gwajin aikin gona da Sin ta tallafa wajen ginawa a gundumar Shamva ta lardin Mashonaland na tsakiyar kasar Zimbabwe da zummar inganta samar da amfanin gona ga manoman kauyuka.
Yankin wanda aka kaddamar jiya Laraba, shi ne irinsa na biyu da masana aikin gona na kasar Sin suka kafa a kasar ta kudancin Afrika, wanda ya samo asali daga gogewar kasar Sin na yaki da talauci da kuma zummar taimakawa manoman kauyuka komawa ga noma domin samun riba, maimakon ciyar da kai kadai.
- HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42
- Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
A cewar masanan na Sin, gomman iyalai ne suke karuwa da shirin aikin gona mai dorewa ta hanyar ingantattun tsare-tsaren ban ruwa da nau’o’in irrai masu jure fari da samar da yabanya da fasahohin noma masu inganta yabanta da tsarin hada kiwo da noma.
Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da yankin da ya samu halartar jami’an kasar Sin da na Zimbabwe da ma manoma, mataimakin ministan kula da filaye da aikin gona da kiwon kifi da albarkatun ruwa da raya kauyuka na kasar Zimbabwe, Vangelis Haritatos, ya ce yankin na bayyana burin kasashen biyu na sauya aikin gona.
A nasa bangare, jakadan Sin a Zimbabwe Zhou Ding, ya ce shirin ya yi daidai da ingantaccen tafarkin Sin na samun ci gaba da ma yaki da talauci. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp