ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Mai Shiga Tsakanin Iyalai Da Masu Garkuwar Jirgin Kasan Kaduna A Masar

by Sulaiman
3 years ago
Kaduna

An kama mai shiga tsakanin Iyalai da masu garkuwar fasinjojin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna wanda aka kaima hari a Kaduna a ranar 28 ga Maris, 2022, Malam Tukur Mamu, a Masar.

Mamu wanda ke rike da sarautar gargajiya ta ‘Dan Iya’ a masarautar Fika a jihar Yobe, an kama shi ne a filin jirgin sama na Alkahira akan hanyarsa ta zuwa kasar Saudiyya.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Saki Karin Mutane 4 Na Jirgin Kasan Abuja-Kaduna

Mamu, shi ne mawallafin jaridar Desert Herald da ke Kaduna, ya fara tattaunawa da ‘yan ta’addan da suka kai hari kan jirgin Abuja zuwa Kaduna, wanda suka yi awon gaba da fasinjoji da dama, bayan fara tattaunawa da su, lamarin ya kai ga sako fasinjoji sama da 20.

ADVERTISEMENT

Daga baya ya janye daga aikin tattaunawar, saboda barazana ga lafiyarsa. Sai dai Mamu ya zama hanyar sadarwa tsakanin ‘yan ta’adda da gwamnati, a wani bangaren kuma tsakanin ‘yan ta’addan da iyalan wadanda aka yi garkuwa da su.

Mamu, ya tabbatar wa manema labarai a ranar Laraba ce wa: “Ina kan hanyata ta zuwa Madina, Kasar Saudiyya ne suka tare ni a filin jirgin sama na Alkahira bisa umarnin gwamnatin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

“Ba a sami wani abu a hannuna ba. Don haka na tabbata jami’an DSS ne suka tura umarnin daga filin jirgin saman Kano, ba ni da abin boyewa kuma kamar yadda na ce ba na jin tsoronsu (DSS).”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN
Labarai

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya
Labarai

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
Next Post
2023: Ba Da Jimawa Ba Za Mu Wallafa Cikakken Sunayen Wadanda Aka Yi Wa Rajistar Katin Zabe – INEC

2023: Ba Da Jimawa Ba Za Mu Wallafa Cikakken Sunayen Wadanda Aka Yi Wa Rajistar Katin Zabe - INEC

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

December 20, 2025
Shugaban Rasha Ya Bayyana Alakar Kasarsa Da Sin A Matsayin Matukar Muhimmanci Ga Samar Da Yanayin Daidaito A Duniya

Shugaban Rasha Ya Bayyana Alakar Kasarsa Da Sin A Matsayin Matukar Muhimmanci Ga Samar Da Yanayin Daidaito A Duniya

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.