ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘An Kashe Mayakan Boko Haram Da Yawa A Wani Hari Da Sojoji Suka Dakile A Neja’

by Sadiq
3 years ago
Sojoji

Gwamnan Jihar Neja, Abubakar Bello, ya ce dakarun sojin Nijeriya sun dakile wani hari da wasu ‘yan tada kayar baya suka kai a wani sansanin soji da ke yankin Sarkin Pawa a jihar.

A cewar NAN, an tabbatar da hakan ne a cikin wata sanarwa da babbar sakatariyar yada labaran gwamnan, Mary Noel-Berje, ta fitar a ranar Litinin.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Ci Rayukan Mutum 4 Tare Da Mamaye Kauyuka 11 A Yobe
  • Kwallon Mata: Nijeriya Ta Yi Rashin Nasara A Hannun Morocco

Bello ya ce maharan sun yi yunkurin kai hari a garin da sansanin sojoji da misalin karfe 2:23 na safiyar ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

Ya ce sojojin da suka amsa kiran gaggawa sun isa garin Sarkin Pawa cikin mintuna 30, kuma an kashe da yawa daga cikin maharan a wani artabu da suka yi.

“Harin da aka shirya zai yi muni idan ba don gaggawar mayar da martani daga jiga-jigan sojojin da ke Sarkin-Pawa da kuma tawagar da suka yi gaggawar amsa kiran gaggawa ba,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

“Ba a samu asarar rayuka a bangaren sojoji ba yayin da aka ce an kashe ‘yan ta’adda da dama yayin da wasu daga cikinsu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

“Amsa kiran gaggawar da sojojin da ke Munya suka yi da kuma martanin da rundunar ta bayar game da kiran da suka yi daga Minna abin yabawa ne.”

Ya yabawa jami’an tsaro bisa kokarin da suke yi na shawo kan lamarin.

“Gwamnatin jihar Neja ta amince da kokarin sojoji da sauran jami’an tsaro wajen yaki da rashin tsaro a jihar,” in ji shi.

Ya kuma tabbatar wa da mazauna jihar cewa jihar na hada hannu da gwamnatin tarayya domin ganin an kawar da masu aikata laifukan da ke kai hare-hare a yankunan manoma da daidaita rayuwar al’umma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Wata Mata Mai Juna Biyu A Jihar Kaduna

'Yan Bindiga Sun Harbe Dan Shekara 7 Bayan Garkuwa Da Mutum 10 A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.